Labarai
Tinubu Ya Nada Gwamna Uba Sani Jakadan Shirin Renewed Hope
Daga Bello Wakili
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani, a matsayin jakadan shirin sabunta kudurori na Renewed Hope kuma mataimakin darakta mai kula da ayyukan jam’iyya da wayar da kai.
Sanarwan hakan ta fito ne daga Fadar shugaban kasa inda ta ce an yi nadin ne bisa la’akari da shugabanci nagari da gwamna Uba Sani ke gudanarwa.
Shugaban kasa Tinubu a matsayinsa na shugaban jam’iyyar APC, ya bukaci gwamnan Kaduna ya taimakawa jam’iyyar wurin wayar da kai da bullo da tsare-tsare a kasa baki daya.
Sanarwan ta ce a matsayinsa na jakadan shirin sabunta kudurori kuma mataimakin darakta, ana sa ran zai kasance kafada-da-kafada da darakta janar na jakadan shirin sabunta kudurori da shugabanin jam’iyyar APC musamman shugaban jam’iyyar APC na kasa, wurin bunkasa dama da daidaito da tsare-tsare a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a kowane mataki.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
