Connect with us

Ilimi

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Published

on

Daga Bello Wakili 

Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da take bayarwa wajen bunƙasa ilimin ‘ya’ya mata.

Karramawar ta kuma yaba da shirye-shiryen da ta aiwatar domin rage mace-macen mata masu juna biyu da jarirai, tare da faɗaɗa tallafin jin ƙai ga iyaye mata da yara a faɗin Nijeriya.

Uwargidan Mataimakin Shugaban Kasa Nana Shettima ce ta wakilci Oluremi Tinubu a babban taron Majalisar ta OAFLAD karo na 29 da na 30 da aka gudanar a Addis Ababa na ƙasar Ethiopia.

OAFLAD, wadda ke aiki ƙarƙashin shirin ta na “We Are Equal”, wato ‘Duk Daya Kuke’, na ci gaba da fafutukar tabbatar da daidaito tsakanin maza da mata, ƙarfafa tattalin arzikin mata, da inganta samun ilimi a faɗin nahiyar Afirka.

Majalisar ta kuma jaddada buƙatar ƙara haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen Afirka domin magance matsalolin da ke addabar mata da yara, musamman a yankunan da rikice-rikice suka shafa.

A jawabinsu  wajen taron, Uwargidan Shugaban Ƙasar Sierra Leone kuma Shugabar OAFLAD, Fatima Maada Bio, tare da Uwargidan Shugaban Ƙasar Ghana, Lordina Mahama, sun yaba wa Sanata Oluremi Tinubu bisa yadda take ci gaba da fafutukar kare haƙƙin mata da yara tare da aiwatar da shirye-shirye masu amfani a Nijeriya da ma wajenta.

Dakta Bio ta jaddada alaƙar da ke tsakanin ci gaba mai ɗorewa da zaman lafiya, inda ta ce ba za a iya tabbatar da cikakken haƙƙin mata ba a wuraren da ke fama da rashin tsaro da rikice-rikice.

Haka kuma, Misis Mahama ta nuna muhimmancin ci gaba da tallafawa ilimin ‘ya’ya mata da kuma ƙarfafa mata masu sana’o’i, a matsayin hanyar gina rayuwa mai ɗorewa.

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara