Connect with us

Ilimi

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Published

on

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ta horas da malamai kan yadda za su gudanar da gwajin karatu da lissafi ga ɗaliban makarantun firamare.

Mai bada  shawara kan tantance ilimin yara a matakin farko na UNICEF Dakta Farouk Aliyu, ya bayyana cewa horon na kwanaki huɗu wanda ya fara a ranar Litinin, na da nufin tantance matsayin yadda dalibai ke koyon karatu a makarantu.

A cewarsa, sun mayar da hankali ne kan ɗaliban aji ɗaya da aji biyu na firamare da kuma malamansu a fannin lissafi da harshen Hausa a kowace makaranta.

Dakta Farouk Aliyu ya ce manufar wannan shiri ita ce samar da hanya mafi sauki da dalibai za su samu ƙwarewar karatu da lissafi a matakin farko a Jihar Jigawa.

Ya ƙara da cewa, ana kuma son fahimtar yadda malamai ke koyarwa tare da tantance ko suna bin hanyoyin koyarwa da UNICEF da sauran hukumomin ilimi suka koyar.

Ya ce idan aka samu gibi, hakan zai sa a sake horas da malamai da tsara manufofi, ko ma sauya tsarin manhajar karatu gaba ɗaya.

Mashawarcin na UNICEF ya ce an horas da mahalarta 67 waɗanda za su tattara sahihan bayanai masu inganci da za su taimaka wajen tsara manufofin da za su tallafa wa tsarin ilimi a jihar.

UNICEF ta dade tana tallafa wa tsarin ilimi a Jigawa da Najeriya baki ɗaya ta hanyar horas da malamai da samar da kayayyakin koyo da koyarwa.

Wannan horon ya ƙara jaddada ƙudirin Kungiyar Tarayyar Turai da gwamnatin Jihar Jigawa wajen inganta sakamakon koyo tare da tabbatar da cewa kowane yaro ya samu ƙwarewar karatu da lissafi tun daga tushe.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an horas da sama da malamai 1,680 na azuzuwan firamare daya zuwa uku, kan hanyoyin koyar da karatu da lissafi  domin inganta koyarwa da samun sakamako mai kyau.

Haka kuma, an raba sama da kayayyakin koyo da koyarwa 152,386 ga ɗaliban matakin farko a makarantun da shirin ya shafa.

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara