Labarai
Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin shugabannin rikon kwarya na kungiyar ‘yan Achaba na yankin.
A Jawabin da ya gabatar a yayin kaddamarwar a fadar Hakimi, Dr Muhammad Uba yace an nada sabbin shugabanin ne domin samun zaman lafiya a tsakanin su.

Ya kuma hore su da su bi dokoki da ka’idojin kungiya, tare da baiwa Karamar hukumar hadin kai da goyan baya wajen kai rahotan zuwan bakin ‘yan achaba dan tabbatar da tsaro.
Builder Muhammed Uba ya ba su tabbacin samun hadin kai da goyan bayan Karamar hukumar, ya kuma nuna rashin jin dadi da yawan sace sacen babura a yankin.

Kazakika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa kokarin sa na tabbatar da tsaro.
Shi ma a nasa jawabin, Hakimin Birnin Kudu Alhaji Hussaini Hassan jibrin ya bada shawarar yiwa Babura lambobi domin samun saukin ganewa tare da basu horo dan kwarewa akan aikin achaba.

A jawaban su daban daban, Shugaban ‘yan achaba na jihar, Abbas Abdulkadir da sakataren kungiyar, Yau Muhammad sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa daukar matakin nada shugabannin riko na kungiyar ‘yan achaba na yankin.
A jawabin sa na godiya, sabon shugaban rikon kungiyar ‘yan Achaba na yankin Auwalu Ibrahim ya bada tabbacin yin aiki bil hakki da gaskiya.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
