Connect with us

Labarai

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Published

on

Daga Bello Wakili 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin ya shafa a ƙauyen Ngoshe da ke Karamar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno.

Shugaban ƙasar ya yi alhinin rasuwar  mutane da ba su ji ba ba su gani ba, ciki har da jami’an soji, da kuma waɗanda suka rasu sakamakon harbin kuskure yayin da jiragen yaƙi ke kai hari ga ‘yan ta’addan da suka tsere.

Ya bayyana harin na ‘yan ta’addan a matsayin mummunan ta’adi da rashin tausayi ga al’umma marasa ƙarfi, tare da kira ga al’ummar Borno da sauran sassan ƙasar da kada su karaya.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa sojojin bisa  martanin gaggawa da suka mayar, wanda ya yi sanadiyyar kashe ‘yan ta’adda da dama tare da tilasta musu janyewa daga yankin.

Ya kuma umarci sojoji da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta  ceto mutanen da ‘yan ta’addan suka sace.

Bugu da ƙari, Shugaban ya umarci rundunar sojoji da ta ƙara ƙaimi wajen kare fararen hula a faɗin ƙasar da kuma hana kai hare-hare kan sansanonin soji musamman a yankin Arewa maso Gabas.

Shugaba Tinubu ya yi addu’ar Allah Ya ji ƙan waɗanda suka rasu a harin da kuma harbin kuskure, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalansu da kuma Gwamnatin Jihar Borno.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara