Labarai
Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin ya shafa a ƙauyen Ngoshe da ke Karamar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno.
Shugaban ƙasar ya yi alhinin rasuwar mutane da ba su ji ba ba su gani ba, ciki har da jami’an soji, da kuma waɗanda suka rasu sakamakon harbin kuskure yayin da jiragen yaƙi ke kai hari ga ‘yan ta’addan da suka tsere.
Ya bayyana harin na ‘yan ta’addan a matsayin mummunan ta’adi da rashin tausayi ga al’umma marasa ƙarfi, tare da kira ga al’ummar Borno da sauran sassan ƙasar da kada su karaya.
Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa sojojin bisa martanin gaggawa da suka mayar, wanda ya yi sanadiyyar kashe ‘yan ta’adda da dama tare da tilasta musu janyewa daga yankin.
Ya kuma umarci sojoji da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta ceto mutanen da ‘yan ta’addan suka sace.
Bugu da ƙari, Shugaban ya umarci rundunar sojoji da ta ƙara ƙaimi wajen kare fararen hula a faɗin ƙasar da kuma hana kai hare-hare kan sansanonin soji musamman a yankin Arewa maso Gabas.
Shugaba Tinubu ya yi addu’ar Allah Ya ji ƙan waɗanda suka rasu a harin da kuma harbin kuskure, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalansu da kuma Gwamnatin Jihar Borno.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
