Connect with us

Labarai

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Published

on

Daga Bello Wakili 

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare ƙasar, tare da tabbatar musu cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da inganta jin daɗinsu da kuma tallafa wa ayyukansu.

Shugaban ya bayar da wannan tabbaci ne yayin wani taron buɗa-baki na mabiya addinin Musulunci da na Kirista da ya yi tare da jami’an Rundunar Sojin ƙasa da sauran hukumomin tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Shugaba Tinubu ya ce taron ya nuna haɗin kan al’ummar Najeriya, yana mai cewa watan Ramadan lokaci ne na yin tunani a kan rayuwa, tsarkake  zuciya da kuma ƙarfafa zaman lafiya tsakanin mabambantan addinai.

Ya yaba wa sojoji kan jajircewarsu wajen kare ƙasa duk da ƙalubalen da suke fuskanta, ciki har da nisantar iyalansu da kuma fuskantar barazanar ‘yan ta’adda da ‘yan Bindiga.

Shugaban ƙasar ya tabbatar musu cewa sadaukarwar da suke yi ba za ta fadi a banza ba, yana mai ƙara cewa jin daɗin sojoji da iyalansu zai ci gaba da kasancewa muhimmin abin da gwamnatinsa za ta bai wa fifiko.

Shugaba Tinubu ya kuma amince da cewa akwai matsalolin ƙarancin gidaje ga sojoji, yana mai cewa gwamnati na aiki tare da sauran masu ruwa da tsaki domin magance matsalar.

Dangane da halin tattalin arzikin ƙasar, shugaban ya bayyana cewa duk da cewa Najeriya ta fuskanci ƙalubale masu tsanani a farkon mulkinsa, matakan da gwamnati ta ɗauka sun fara haifar da Da mai ido.

Ya bayyana kwarin gwiwa cewa ƙasar ta fara fita daga mawuyacin hali na tattalin arziki, tare da bada tabbacin cewa nan gaba kadan za a kara ganin canji mai ma’ana a Najeriya.

Shugaban ƙasar ya kuma miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno kan wani sabon lamari na rashin tsaro da ya faru a jihar, yana mai cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da tallafa wa ƙoƙarin da ake yi domin kawo ƙarshen ta’addanci da ‘yan bindiga a faɗin ƙasar.

Tun da farko, Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya gode wa shugaban ƙasa bisa shirya taron buɗa-bakin na haɗin gwiwar addinai, tare da yaba masa kan amincewa da matakan da nufinsu shi ne inganta jin daɗin jami’an rundunar soji.

Ya kuma yaba wa shugaban ƙasan kan amincewa da ƙarin albashi ga sojoji, ƙarin alawus ga rundunar Brigade of Guards, da kuma amincewa da sayen sabbin kayan aiki da inganta matsugunan sojoji.

Laftanar Janar Shaibu ya ce waɗannan matakai za su taimaka matuƙa wajen ƙara inganta aikin rundunar da kuma ƙarfafa gwiwar jami’anta.

Haka kuma ya sake jaddada biyayyar rundunar sojin ƙasa ga shugaban ƙasa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen kare dimokuraɗiyyar Najeriya da kuma martabar ƙasar.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara