Labarai
Gwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
Gwamnatin Jihar Zamfara ta ayyana dokar ta-baci kan cutar shan-inna a Karamar Hukumar Gummi domin dakile yaduwar cutar da kuma kara karfafa ayyukan rigakafi.
Kwamishinar Lafiya ta jihar, Dakta Nafisa Muhammad Maradun, ta bayyana hakan a taron wata-wata na kwamitin kula da harkokin kiwon lafiya na matakin farko da aka gudanar a ofishin Mataimakin Gwamnan jihar a Gusau.
Ta ce matakin zai taimaka wajen kara sa ido kan cutar, fadada shirin allurar rigakafi da kuma wayar da kan al’umma domin hana yaduwar ta.
Mataimakin Gwamnan jihar, Mani Mallam Mummuni, ya jaddada muhimmancin allurar rigakafi wajen kare lafiyar jama’a musamman yara.
Ya kuma bayyana cewa a watan Maris za a gudanar da gangamin allurar rigakafin shan-inna wanda ake sa ran zai kai ga sama da yara miliyan daya da dubu dari uku a fadin jihar.
Haka kuma ya bukaci hukumomin lafiya su tabbatar da cewa alluran sun isa ga yaran da aka tsara su karba.
Shi ma mai kula da ayyukan Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) a jihar, Dakta Raji Mukhtar, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da bai wa gwamnatin Zamfara goyon baya wajen kawo karshen cutar shan-inna.
Aminu Dalhatu/Gusau
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
