Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi

Published

on

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ayyana dokar ta-baci kan cutar shan-inna a Karamar Hukumar Gummi domin dakile yaduwar cutar da kuma kara karfafa ayyukan rigakafi.

 

Kwamishinar Lafiya ta jihar, Dakta Nafisa Muhammad Maradun, ta bayyana hakan a taron wata-wata na kwamitin kula da harkokin kiwon lafiya na matakin farko da aka gudanar a ofishin Mataimakin Gwamnan jihar a Gusau.

 

Ta ce matakin zai taimaka wajen kara sa ido kan cutar, fadada shirin allurar rigakafi da kuma wayar da kan al’umma domin hana yaduwar ta.

 

Mataimakin Gwamnan jihar, Mani Mallam Mummuni, ya jaddada muhimmancin allurar rigakafi wajen kare lafiyar jama’a musamman yara.

 

Ya kuma bayyana cewa a watan Maris za a gudanar da gangamin allurar rigakafin shan-inna wanda ake sa ran zai kai ga sama da yara miliyan daya da dubu dari uku a fadin jihar.

 

Haka kuma ya bukaci hukumomin lafiya su tabbatar da cewa alluran sun isa ga yaran da aka tsara su karba.

 

Shi ma mai kula da ayyukan Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) a jihar, Dakta Raji Mukhtar, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da bai wa gwamnatin Zamfara goyon baya wajen kawo karshen cutar shan-inna.

Aminu Dalhatu/Gusau

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara