Connect with us

Labarai

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Published

on

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na Musamman Kan Kudi domin tsara tsarin samun kudade mai dorewa ga shirye-shiryen abinci mai gina jiki a fadin Najeriya.

An kafa wannan kwamiti ne a yayin wani taron yanar gizo na Majalisar, inda ake sa ran zai gabatar da taswirar tsarin kudi cikin kwanaki 30 ga NCN da kuma Majalisar Tattalin Arzikin Kasa domin nazari da amincewa.

Kwamiti, wanda Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ke jagoranta, ya kunshi Ministocin Ilimi, Harkokin Ruwa, Harkokin Mata, da Kimiyya da Fasaha, tare da Mataimakin Babban Sakataren Fadar Shugaban Kasa da Babban Mataimakin Musamman kan Lafiya.

Ma’aikatar Kasafi da Shirye-shiryen Tattalin Arziki za ta kasance sakatariya ta wannan kwamitim.

Mataimakin Shugaban Kasa, Shettima, ya jaddada bukatar ajiyar kudade na musamman domin shirye-shiryen abinci da gina jiki, don tabbatar da cewa kudaden da aka ware a kasafin kudi suna haifar da ingantattun canje-canje a rayuwar ‘yan Najeriya.

Ya kuma yi kira da a gaggauta wucewa da Dokar Abinci da Gina Jiki ta Kasa domin samar da tsarin doka da na hukuma mai karfi na hadin kai, samun kudade da kuma alhakin gudanarwa a fadin sassa daban-daban.

Mataimakin Shugaban Kasa ya bukaci Ma’aikatun, Sassa da Hukumomi su tabbatar cewa kudaden da aka amince da su don shirye-shiryen abinci da gina jiki ana sakin su kuma ana amfani da su yadda ya kamata.

Haka kuma, ya karfafa gwamnatocin jihohi su gaggauta aiwatar da shirin domin magance gibin ayyuka a jihohin da ke fama da karancin abinci mai gina jiki.

Bello Wakili

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara