Labarai
Shugaban Majalisar Wakilai Dr. Abbas ya Tallafawa Aikin Raya Kasa da Ake Yi a Lere da Naira Miliyan 5
Shugaban Majalisar Wakilai ya jadda da kudurin Majalisar Dokokin Kasa na tallafawa Kungiyoyin raya al’umma.
Shugaban Majalisar Wakilai Dr. Tajuddeen Abbas, ya jadda da kudurin Majalisar Dokokin Kasa wajen tallafawa ayyukan da Kungiyoyin raya al’umma suka aiwatar a fadin Kasar Nan.
Dr. Tajuddeen Abbas ya ambata haka ne, lokacin taron kaddamar da kalandar (ALMANAC) na Kungiyar raya garin Lere watau Lere Development Association (LDA) na shekara ta 2026, Wanda aka Yi a Lere ta Jihar Kaduna.
Kakakin Majalisar Wanda Hon. Alhassan Ado Doguwa ya wakilci shi a wajen taron, ya ce Majalisar Dokokin Kasa ta himmatu wajen yin Dokoki da zasu baiwa Kungiyoyi damar aiwatar da ayyukan Kawu cigaba ga al’ummominsu.
Ya Yi bayanin cewa, Gwamnati Mai ci tana aiki kafada da kafada da al’ummomin Kasar Nan wajen maido da zaman Lafiya da tsaro a Kasa.
Dr. Tajuddeen Abbas ya karfafa guiwar Kungiyar ta Lere Development Association LDA ta cigaba da tallafawa kokarin Gwamnati wajen aiwatar da manufofinta da suka shafi rayuwar Yan Nigeria Kai Tsaye.
Kazalika, Shugaban Majalisar ya baiwa Kungiyar ta raya garin Lere gudunmawar Naira Miliyan Biyar domin cigaba da gudanar da hidimominta.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Karamar Hukumar LERE, Alhaji Jafar Ahmed ya bukaci Kungiyoyin raya al’umma su kirkiro shirye shiryen da zasu taimakawa Gwamnati wajen samar da guraban aikin yi ga Matasa.
Ya yabawa Kungiyar LERE Development Association LDA bisa yadda take Jan ragamar aiwatar da ayyukan raya Kasa a yankin.

Tun farko sai da Mai Martaba Sarkin LERE, Engr. Sulaiman Umaru, ya bayyana godiyarsa bisa yadda Shugaban Majalisar yake taimakawa al’ummomin Kasar Nan.
An gudanar da raye rayen al’adun gargajiya a wajen taron Wanda ya Sami halartan mashahuran Yan Nigeria.
COV/Sani Lere
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
