Labarai
Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN
Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida na zama babbar barazana ga ƙwarewa da amincewar jama’a da kuma zaman lafiyar ƙasa.
A cikin sakon sabuwar shekara da ya aikewa ’yan jarida, Sarkinfada ya gargaɗi cewa yaɗa labaran ƙarya da rashin kwaklwaran binciken jarida da kuma ayyukan mutanen da ba su da horo amma suke kiran kansu ’yan jarida, na lalata martabar aikin jarida tare da raunana ayyukan sahihan ’yan jarida.
Ya bayyana cewa rahotannin da ba a tantance ba kuma masu tayar da hankali, musamman kan muhimman batutuwan ƙasa, na iya haddasa firgici, yaɗa bayanan ƙarya da kuma tashin hankalin al’umma, yayin da ayyukan marasa ƙwarewa ke bata sunan ’yan jarida masu bin ka’ida.
Shugaban NUJ ya yi kira ga ’yan jarida da su sake tsayawa tsayin daka kan ɗabi’un aikin jarida, yana jaddada muhimmancin sahihanci, daidaito, tantance gaskiya da yin cikakken bincike bisa manufofin NUJ da ƙa’idar aiki.
Ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ƙarfafa hanyoyin sa-ido na cikin gida tare da bada horo na ci gaba mai muhimmanci, yayin da ya shawarci jama’a da su yi dogara ga sahihan hanyoyin labarai tare da tantance bayanai kafin su yaɗa su.
Sarkinfada ya sake jaddada kudurin reshen NUJ FRCN Kaduna na inganta ƙwarewa da mutuncin kafafen yaɗa labarai, yana bayyana sabuwar shekarar a matsayin wata dama ta sabunta jajircewa ga aikin jarida mai inganci a Najeriya.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
