Connect with us

Labarai

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Published

on

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida na zama babbar barazana ga ƙwarewa da amincewar jama’a da kuma zaman lafiyar ƙasa.

A cikin sakon sabuwar shekara da ya aikewa ’yan jarida, Sarkinfada ya gargaɗi cewa yaɗa labaran ƙarya da rashin kwaklwaran binciken jarida da kuma ayyukan mutanen da ba su da horo amma suke kiran kansu ’yan jarida, na lalata martabar aikin jarida tare da raunana ayyukan sahihan ’yan jarida.

Ya bayyana cewa rahotannin da ba a tantance ba kuma masu tayar da hankali, musamman kan muhimman batutuwan ƙasa, na iya haddasa firgici, yaɗa bayanan ƙarya da kuma tashin hankalin al’umma, yayin da ayyukan marasa ƙwarewa ke bata sunan ’yan jarida masu bin ka’ida.

Shugaban NUJ ya yi kira ga ’yan jarida da su sake tsayawa tsayin daka kan ɗabi’un aikin jarida, yana jaddada muhimmancin sahihanci, daidaito, tantance gaskiya da yin cikakken bincike bisa manufofin NUJ da ƙa’idar aiki.

Ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ƙarfafa hanyoyin sa-ido na cikin gida tare da bada horo na ci gaba mai muhimmanci, yayin da ya shawarci jama’a da su yi dogara ga sahihan hanyoyin labarai tare da tantance bayanai kafin su yaɗa su.

Sarkinfada ya sake jaddada kudurin reshen NUJ FRCN Kaduna na inganta ƙwarewa da mutuncin kafafen yaɗa labarai, yana bayyana sabuwar shekarar a matsayin wata dama ta sabunta jajircewa ga aikin jarida mai inganci a Najeriya.

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara