Connect with us

Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kasafin 2026

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sanya hannu kan dokar Kasafin Kuɗin Shekarar 2026, bayan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ta amince da shi.

An gudanar da bikin sanya hannun ne a Fadar Gwamnati da ke Gusau.

Sai dai a wajen taron, gwamnan bai bayyana jimillar adadin kasafin kuɗin shekarar ta 2026 ba.

Tun a ranar 4 ga watan Disamba ne Gwamna Dauda Lawal ya gabatar da kasafin kuɗi da ya haura naira biliyan 861 na shekarar 2026 ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara domin amincewa.

Manyan jami’an da suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Mani Malam Mumini; Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Bilyaminu Isma’il Moriki; Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG); Shugaban Ma’aikata (Chief of Staff); kwamishinoni da sauran manyan jami’an gwamnati.

 

A baya, Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ta riga ta amince da Kudirin Kasafin Kuɗin 2026 ya zama doka, bayan gabatar da rahoton Kwamitin Majalisar kan Kuɗi da Kasafi.

Kudirin ya tanadi jimillar kasafin kuɗi na naira biliyan 871.337 domin shekarar  2026.

Yayin gabatar da rahoton kwamitin, Shugaban Kwamitin, Rilwanu Marafa Na Gambo, ya bayyana cewa dukkan Ma’aikatun Gwamnati, Hukumomi da Cibiyoyi (MDAs) a jihar sun bayyana gaban kwamitin tare da kare kasafin kuɗinsu. Ya ƙara da cewa an samu gagarumin ci gaba a tsarin samun kuɗaɗen shiga na yawancin hukumomi.

Na Gambo ya kuma bayyana cewa kwamitin ya ba da shawarar ƙara naira biliyan 8 domin ayyukan ci gaba (capital expenditure) a Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, tare da ƙara naira biliyan 2 domin kuɗaɗen gudanarwa (recurrent expenditure) ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara.

A lokacin amincewa da kudirin, Shugaban Majalisar, Bilyaminu Isma’il Moriki, ya ce Majalisar ta yi la’akari da manyan abubuwan da ya kamata gwamnati ta fi bai wa fifiko yanzu, da suka haɗa da tsaro, noma, lafiya, ilimi da gine-gine.

Ya ce an tsara kasafin kuɗin ne domin ya dace da buƙatu da muradun al’umma a matakin ƙananan hukumomi da sauran fannoni, tare da tabbatar da daidaiton kasafi da mai da hankali sosai kan adalci da haɗa kowa da kowa.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara