Connect with us

Ilimi

An Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman Gumel, ya bayyana sabon Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Dutse, Farfesa Ahmad Muhammed Gumel, a matsayin mutum mai son kawo cigaba ga al’ummarsa.

Mataimakin Gwamnan ya bayyana hakan ne a wurin liyafar karramawa da abokan Farfesa Gumel suka shirya masa a dakin taro na masarautar Gumel.

A cewarsa, bai yi mamakin yadda jama’a suka halarci bikin rantsar da Shugaban Jami’ar a Dutse da kuma liyafar da aka yi masa a Gumel ba, domin sabon Shugaban Jami’ar mutum ne mai kula da jama’a, abokan aikinsa da duk wanda ya taɓa hulɗa da shi.

Ya kuma bayyana cewa a lokacin da Farfesa Gumel yake ƙasar Malaysia, ya taimaka wajen samar wa da dama daga cikin mutanensa guraben karatu da tallafin karatu.

 

Ya buƙaci sabon Shugaban Jami’ar da ya kasance mai aiki bisa gaskiya, tare da yin adalci ga kowa, yana mai cewa yana da yaƙinin  zai yi nasara a Jami’ar Tarayya da ke Dutse.

Dr. Najib Abdulhamid, wanda ke aiki da Microsoft Office a ƙasar Kenya, ya yi magana a madadin abokan sabon Shugaban Jami’ar, inda ya ce suna farin cikin ganin abokinsu tun daga yarinta ya kai kololuwar matsayinsa na aiki, kuma za su tallafa masa da addu’o’i da shawarwari domin ya zamto abin tunawa a tarihin jami’ar.

Ya ce sun yi nazari sosai kan tsare-tsarensa guda goma sha ɗaya, kuma suna da yaƙinin cewa zai  mayar da hankali, jajircewa da kuma samun ƙwararrun ma’aikata, domin cimma manufofinsa, ya ce za kuma su yi amfani da alaƙarsu wajen taimaka masa ya cimma burinsa ga jami’ar.

A nasa jawabin, Farfesa Muhammed Sani Gumel, tsohon Mataimakin Shugaban Jami’a mai kula da harkokin karatu a Jami’ar Bayero da ke Kano, ya taya sabon Shugaban Jami’ar murna tare da ba shi shawarar fahimtar dokokin jami’a sosai.

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara