Connect with us

Labarai

Hukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo

Published

on

Daga Yusuf Zubairu/Abubakar Hamza 

Shugaban Hukumar Raya Kogin Benuwe Dakta Mahmud Sanusi Mohammed, ya bullo da wata fasaha mai sauki da za ta kare hanyar shiga aikin ban-ruwa na Tafkin Geriyo daga zaizayewa  a lokacin damina.

Wannan shiri ya biyo bayan ziyarar duba aikin samar da ruwa ga gonaki  da ya kai, inda ya tantance matsalolin da ke haddasa zaftarewar hanyoyi musamman hanyar da ake wannan aiki.

   A tsakiya, Shugaban Hukumar Raya Kogin Benuwe ne Dakta Mahmud Sanusi Mohammed

Domin magance matsalar, hukumar na amfani da wata sabuwar hanya wadda ta haɗa da amfani da tsofaffin tayoyin motoci da aka cika da dakakken dutse da tsakuwa. Ana jera tayoyin ne ta yadda za su matse juna, su zama wani gini mai ƙarfi domin hana zaizayar ƙasa da kuma daidaita magudanar ruwa.

An tsara wannan dabara ce domin rage ƙarfin ruwan da ke gudana a saman ƙasa, ƙarfafa ƙasa, da kuma hana zaftarewar hanya a lokacin damina.

Jami’ai sun bayyana cewa wannan hanya da aka bullo da ita tana da amfani matuka ga muhalli, domin tana ƙarfafa sake amfani da kayayyakin shara,  tare da rage kuɗaɗen da ake kashewa wajen yin gyara.

Haka kuma ana sa ran wannan tsari zai ƙara ingancin hanyar shiga wurin tare da tabbatar da samun damar zuwa wuraren ban-ruwa a kowane lokaci na shekara.

Shugaban Hukumar ya shaidawa Rediyon Najeriya cewa,halin yanzu wannan aiki a cigaba da gudana, wanda ke nuna ƙudurin shugabancin hukumar na samar da mafita da za ta kare muhimman kayayyakin more rayuwa, tare da ƙarfafa ayyukan ban-ruwa masu dorewa a yankin.

Labarai

Labarai17 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara