Connect with us

Labarai

An Tsinci Gawar Wani Mutum A Cikin Rijiya A Karamar Hukumar Gezawa

Published

on

Al’ummar kauyen Babawa da ke karamar hukumar Gezawa a Kano sun shiga cikin firgici bayan da aka tsinci wani mutum mai kimanin shekaru 45 a cikin rijiya.

Saminu Yusif Abdullahi jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran gaggawa daga ASP Kabiru Lawan na rundunar ‘yan sandan Gezawa.

Saminu ya yi nuni da cewa, tawagar ceto ta yi nasarar zakulo mutumin daga rijiyar kuma daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsa.

Sai dai, ya jaddada cewa, har yanzu ba a san ko wanen ba, saboda shugabannin al’umma da mazauna yankin sun ce ba su gane shi ba, ba su kuma san daga inda ya fito ba.

Hakazalika, mutane uku sun makale a lokacin da suke aikin hako rijiya a kauyen Gargajiga da ke karamar hukumar Minjibir.

Saminu ya kara da cewa hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ceto mutum biyu da ransu, yayin da aka dauko mutum na uku Yusuf Nadabo mai shekaru 50 da haihuwa, a sume, daga bisani kuma aka tabbatar da mutuwarsa.

Jami’in hulda da jama’an ya yi nuni da cewa, wani iftila’in ya sake afkuwa a Kano inda wata mummunar gobara ta kona shaguna da dama a kan titin Ibrahim Taiwo, inda aka ciro wani mutum a sume, yayin da aka yi asarar dukiyoyi na miliyoyin naira.

Daga Khadija Aliyu

Labarai

Labarai17 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara