Labarai
An Tsinci Gawar Wani Mutum A Cikin Rijiya A Karamar Hukumar Gezawa
Al’ummar kauyen Babawa da ke karamar hukumar Gezawa a Kano sun shiga cikin firgici bayan da aka tsinci wani mutum mai kimanin shekaru 45 a cikin rijiya.
Saminu Yusif Abdullahi jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran gaggawa daga ASP Kabiru Lawan na rundunar ‘yan sandan Gezawa.
Saminu ya yi nuni da cewa, tawagar ceto ta yi nasarar zakulo mutumin daga rijiyar kuma daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsa.
Sai dai, ya jaddada cewa, har yanzu ba a san ko wanen ba, saboda shugabannin al’umma da mazauna yankin sun ce ba su gane shi ba, ba su kuma san daga inda ya fito ba.
Hakazalika, mutane uku sun makale a lokacin da suke aikin hako rijiya a kauyen Gargajiga da ke karamar hukumar Minjibir.
Saminu ya kara da cewa hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ceto mutum biyu da ransu, yayin da aka dauko mutum na uku Yusuf Nadabo mai shekaru 50 da haihuwa, a sume, daga bisani kuma aka tabbatar da mutuwarsa.
Jami’in hulda da jama’an ya yi nuni da cewa, wani iftila’in ya sake afkuwa a Kano inda wata mummunar gobara ta kona shaguna da dama a kan titin Ibrahim Taiwo, inda aka ciro wani mutum a sume, yayin da aka yi asarar dukiyoyi na miliyoyin naira.
Daga Khadija Aliyu
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
