Connect with us

Labarai

An Tsinci Gawar Wani Mutum A Cikin Rijiya A Karamar Hukumar Gezawa

Published

on

Al’ummar kauyen Babawa da ke karamar hukumar Gezawa a Kano sun shiga cikin firgici bayan da aka tsinci wani mutum mai kimanin shekaru 45 a cikin rijiya.

Saminu Yusif Abdullahi jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran gaggawa daga ASP Kabiru Lawan na rundunar ‘yan sandan Gezawa.

Saminu ya yi nuni da cewa, tawagar ceto ta yi nasarar zakulo mutumin daga rijiyar kuma daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsa.

Sai dai, ya jaddada cewa, har yanzu ba a san ko wanen ba, saboda shugabannin al’umma da mazauna yankin sun ce ba su gane shi ba, ba su kuma san daga inda ya fito ba.

Hakazalika, mutane uku sun makale a lokacin da suke aikin hako rijiya a kauyen Gargajiga da ke karamar hukumar Minjibir.

Saminu ya kara da cewa hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ceto mutum biyu da ransu, yayin da aka dauko mutum na uku Yusuf Nadabo mai shekaru 50 da haihuwa, a sume, daga bisani kuma aka tabbatar da mutuwarsa.

Jami’in hulda da jama’an ya yi nuni da cewa, wani iftila’in ya sake afkuwa a Kano inda wata mummunar gobara ta kona shaguna da dama a kan titin Ibrahim Taiwo, inda aka ciro wani mutum a sume, yayin da aka yi asarar dukiyoyi na miliyoyin naira.

Daga Khadija Aliyu

Labarai

Labarai13 hours ago

Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro

Daga Aliyu Muraki  Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce gwamnonin Arewa sun amince su sayi na’urorin zamani na...

Labarai14 hours ago

‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma

Daga Nasir Malali An kashe ’yan bindiga guda goma sha takwas a wani samame da Rundunar Hadin Gwiwa ta Operation...

Labarai15 hours ago

Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda

Daga Isma’il Adamu Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa tana da kwarin gwiwar lashe karin mukaman siyasa a zaben shekarar 2027,...

Labarai15 hours ago

ASUU-SSU Ta Zargi VC Da Kary Dokokin Jami’ar Jihar Sakkwato

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin...

Labarai17 hours ago

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda

Daga Bello Wakili Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ganawar sirri da gwamnonin jihohi shidda daga sassan ƙasar a...

Labarai22 hours ago

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara

Daga Bello Wakili Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya isa Abidjan na kasar Côte d’Ivoire, domin wakiltar Shugaban Kasa Bola...

Labarai2 days ago

Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini

Majalisar Dokokin Amurka ya iso Abuja yayin da ƙasashen biyu ke ƙara matsa ƙaimi wajen tattaunawar diflomasiyya kan haɗin gwiwar...

Labarai2 days ago

Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki

Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta bayyana cewa ta dakile wani yunkurin juyin mulki, bayan da wasu sojojin ƙasar suka sanar da...

Labarai2 days ago

Jirgin Sojin Saman Najeriya Ya Yi Wani  Hatsari a Neja

Wani jirgin Sojin saman Najeriya ya yi haɗari jim kaɗan bayan tashi daga sansanin Sojin ƙasar da ke Kainji a...

Labarai3 days ago

Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161

Daga Usman Muhammad Zaria Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jihar Jigawa ta yi kiyasin kashe kudade miliyan dubu 161 da...

Mafi Shahara