Labarai
An Tsinci Gawar Wani Mutum A Cikin Rijiya A Karamar Hukumar Gezawa
Al’ummar kauyen Babawa da ke karamar hukumar Gezawa a Kano sun shiga cikin firgici bayan da aka tsinci wani mutum mai kimanin shekaru 45 a cikin rijiya.
Saminu Yusif Abdullahi jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran gaggawa daga ASP Kabiru Lawan na rundunar ‘yan sandan Gezawa.
Saminu ya yi nuni da cewa, tawagar ceto ta yi nasarar zakulo mutumin daga rijiyar kuma daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsa.
Sai dai, ya jaddada cewa, har yanzu ba a san ko wanen ba, saboda shugabannin al’umma da mazauna yankin sun ce ba su gane shi ba, ba su kuma san daga inda ya fito ba.
Hakazalika, mutane uku sun makale a lokacin da suke aikin hako rijiya a kauyen Gargajiga da ke karamar hukumar Minjibir.
Saminu ya kara da cewa hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ceto mutum biyu da ransu, yayin da aka dauko mutum na uku Yusuf Nadabo mai shekaru 50 da haihuwa, a sume, daga bisani kuma aka tabbatar da mutuwarsa.
Jami’in hulda da jama’an ya yi nuni da cewa, wani iftila’in ya sake afkuwa a Kano inda wata mummunar gobara ta kona shaguna da dama a kan titin Ibrahim Taiwo, inda aka ciro wani mutum a sume, yayin da aka yi asarar dukiyoyi na miliyoyin naira.
Daga Khadija Aliyu
-
Labarai4 days agoShettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
-
Labarai2 days agoTawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
-
Labarai3 days agoMa’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
-
Labarai6 days agoShugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
-
Labarai2 days agoFadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
-
Labarai7 days agoShugaba Tinubu Ya Nada Janar Christopher Musa Sabon Ministan Tsaro
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
-
Labarai15 hours agoASUU-SSU Ta Zargi VC Da Kary Dokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
