Ilimi
Dalibar Jami’ar Bayero Daga Jihar Jigawa ta Sami Lambobin Yabo a Fannin Ilimin Kimiyyar Magunguna
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamna Umar Namadi ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ba da kulawa, ƙarfafawa da tallafawa fitattun ‘yan asalin jihar a fannoni daban-daban na Ilimi.
Ya bayyana hakan ne yayin da yake karrama wata fitacciyar ‘yar asalin Jigawa, Maryam Sulaiman Abubakar, wadda ta kammala karatun a fannin kimiyyar magunguna(Pharmacy) a Jami’ar Bayero da ke Kano, a zauren Majalisar Gwamnati da ke Fadar Gwamnati, Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa karfafa wadanda suka nuna hazaka na daga cikin ginshiƙan hangen nesan gwamnatinsa wajen tabbatar da ci gaba mai ɗorewa.
Da yake gabatar da wadda aka karrama, Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ya bayyana cewa Maryam Sulaiman ta yi fice sosai a fannin karatunta, inda ta lashe kusan dukkanin lambobin yabo da jami’ar ta bayar a ffannin kimiyyar magunguna wato pharmacy.

A cewarsa, nasarorin da ta samu sun nuna ƙwazo, jajircewa da kuma ƙwarewa a fannin ilimi.
Ya ce Maryam Sulaiman ta samu lambar yabo ta ƙwararryar ɗalibar da ya kammala karatun Pharm D gaba ɗaya, da lambar yabo ta kungiyar masana kimiyyar magunguna ta kasa wato Pharmacy Council of Nigeria, da kungiyar mata masana kimiyyar magunguna wato Association of Lady Pharmacists, da kuma ta Clinical Pharmacists Association of Nigeria.
Sauran lambobin yabon sun haɗa da na Association of Hospital and Administrative Pharmacists of Nigeria, da kuma lambar yabo ta ƙwarewa daga Pharmacist Ahmed Ghana a matsayin mafi ƙwararriyar ɗalibar da ta kammala karatu daga Jihar Jigawa.
Gwamna Namadi ya taya Maryam murnar wannan gagarumar nasara ta ilimi, wadda ya bayyana a matsayin abin koyi da alfahari.
Ya gode wa Allah da ya albarkaci Jihar Jigawa da hazikan matasa kamar Maryam Sulaiman, yana mai cewa ta nuna bajinta ta musamman ta hanyar lashe manyan lambobin yabo da kuma samun kusan cikakkun maki a karatunta.

“Muna alfahari da ke, kuma muna jin daɗin kasancewarki ‘yar asalin Jihar Jigawa. Nasarorinki sun sa mu alfahari.”
Namadi ya kuma nuna cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa mata domin girmama baiwar da take da ita ta musamman.
Ya ce gwamnatin jihar za ta ɗauki nauyin karatunta gaba ɗaya har zuwa matakin digirin digirgir.
Har ila yau, Namadi ya umarci Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da ta gaggauta sauƙaƙa mata samun gurbin karatu domin ci gaba da karatunta.
Ya sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da zuba jari a fannin ilimi tare da tallafawa fitattun ‘yan asalin Jigawa, a matsayin wata hanya ta gina al’umma mai ilimi, da dogaro da kai.
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
