Connect with us

Fasaha

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025

Published

on

Hukumar shirya jarabawar ta kasa NECO ta fitar da jarabawar SSCE dalibai dubu 818, 492 suka sami kiridit 5 zuwa sama da suka hada darasin Ingilishi da Lissafi.

 

Adadin bisa ga sakamakon ya nuna dalibai kashi sittin da biyu sun smai nasara.

 

Magatakardar NECO kuma Babban Jami’in Hukumar, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a lokacin da yake fitar da sakamakon jarabawar SSCE na shekarar 2025 a hedkwatar NECO da ke Minna babban birnin Jihar Neja.

 

Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ya bayyana cewa adadin dalibai miliyan daya da dubu dari da arba’in da hudu da dubu dari hudu da casa’in da shida da ke wakiltar maki tamanin da hudu da suka zana jarrabawar sun samu kiridit 5 ko sama da haka ba tare da la’akari da harshen Ingilishi da lissafi ba.

 

A cewar Farfesa Danteni “. A yayin gudanar da jarrabawar kammala sakandare ta shekarar 2025, (SSCE), an gano makarantu talatin da takwas suna yin magudin zabe) a jihohi talatin, yana mai jaddada cewa, za a gayyace su zuwa majalisar domin tattaunawa, bayan haka za a sanya takunkumin da ya dace.

 

Shugaban Hukumar NECO ya yi nuni da cewa an ba manya jami’ai Tara, Uku a Kogi, Daya a Niger, Uku a F.C.T, Daya a Kano da Daya a Jihohin Osun takardar gargadi saboda rashin kulawar da ake yi, wanda ya sa aka samu makara, rashin da’a, cin zarafi, da rashin biyayya.

 

Ya ce a lokacin Jarrabawar an samu rikicin kabilanci wanda ya haifar da bullar takardun jarrabawar a Jihar Adamawa daga ranar 7 zuwa 25 ga watan Yulin 2025 da ya shafi makarantu Takwas (8), inda ya ce jimillar darussa goma sha uku da takardu ashirin da tara (29) ne wannan lamarin ya shafa, sannan kuma dalibai dari biyar da casa’in da tara ne abin ya shafa.

 

NECO ta fara tattaunawa da jihar Adamawa da nufin gudanar da jarrabawar makarantun da abin ya shafa, inda ya nuna cewa ba za a iya fitar da sakamakon makarantun takwas a yanzu ba.” Inji magatakardan NECO.

 

Farfesa Dantani Wushishi ya bayyana cewa an fitar da sakamakon jarrabawar cikin gida na SSCE kwanaki hamsin da hudu bayan rubuta na karshe a watan Agusta, 2025, wanda ke nuni da cewa an kammala dukkan matakan da suka kai ga samun nasarar fitar da sakamakon cikin gida na 2025 SSCE.

 

Ya kara da cewa, fitar da sakamakon na cikin 2025 na SSCE cikin sauki, shaida ne na ma’aikatan Hukumar Jarrabawar bisa kwarewa, da’a da kuma ci gaba da neman nagartarsu, da sanin ya kamata, da kula da inganci, da jajircewa wajen bin ka’idojin da’a, sun tabbatar da cewa NECO ta samar da sakamakon da ya dace kuma dalibai, cibiyoyi da sauran jama’a suka amince da su.

 

 

Farfesa Dantani ya bayyana matukar godiya ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinuba bisa jajircewarsa wajen ganin an inganta ilimi ya samar da kyakkyawan yanayi ga hukumar NECO ta samu ci gaba, ya kuma yabawa ministan ilimi Dr Maruf Tunji Alyssa da karamin ministan ilimi Farfesa Suwaiba Said Ahmad bisa goyon baya da fahimtarsu.

 

COV ALIYU LAWAL.

 

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara