Connect with us

Fasaha

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025

Published

on

Hukumar shirya jarabawar ta kasa NECO ta fitar da jarabawar SSCE dalibai dubu 818, 492 suka sami kiridit 5 zuwa sama da suka hada darasin Ingilishi da Lissafi.

 

Adadin bisa ga sakamakon ya nuna dalibai kashi sittin da biyu sun smai nasara.

 

Magatakardar NECO kuma Babban Jami’in Hukumar, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a lokacin da yake fitar da sakamakon jarabawar SSCE na shekarar 2025 a hedkwatar NECO da ke Minna babban birnin Jihar Neja.

 

Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ya bayyana cewa adadin dalibai miliyan daya da dubu dari da arba’in da hudu da dubu dari hudu da casa’in da shida da ke wakiltar maki tamanin da hudu da suka zana jarrabawar sun samu kiridit 5 ko sama da haka ba tare da la’akari da harshen Ingilishi da lissafi ba.

 

A cewar Farfesa Danteni “. A yayin gudanar da jarrabawar kammala sakandare ta shekarar 2025, (SSCE), an gano makarantu talatin da takwas suna yin magudin zabe) a jihohi talatin, yana mai jaddada cewa, za a gayyace su zuwa majalisar domin tattaunawa, bayan haka za a sanya takunkumin da ya dace.

 

Shugaban Hukumar NECO ya yi nuni da cewa an ba manya jami’ai Tara, Uku a Kogi, Daya a Niger, Uku a F.C.T, Daya a Kano da Daya a Jihohin Osun takardar gargadi saboda rashin kulawar da ake yi, wanda ya sa aka samu makara, rashin da’a, cin zarafi, da rashin biyayya.

 

Ya ce a lokacin Jarrabawar an samu rikicin kabilanci wanda ya haifar da bullar takardun jarrabawar a Jihar Adamawa daga ranar 7 zuwa 25 ga watan Yulin 2025 da ya shafi makarantu Takwas (8), inda ya ce jimillar darussa goma sha uku da takardu ashirin da tara (29) ne wannan lamarin ya shafa, sannan kuma dalibai dari biyar da casa’in da tara ne abin ya shafa.

 

NECO ta fara tattaunawa da jihar Adamawa da nufin gudanar da jarrabawar makarantun da abin ya shafa, inda ya nuna cewa ba za a iya fitar da sakamakon makarantun takwas a yanzu ba.” Inji magatakardan NECO.

 

Farfesa Dantani Wushishi ya bayyana cewa an fitar da sakamakon jarrabawar cikin gida na SSCE kwanaki hamsin da hudu bayan rubuta na karshe a watan Agusta, 2025, wanda ke nuni da cewa an kammala dukkan matakan da suka kai ga samun nasarar fitar da sakamakon cikin gida na 2025 SSCE.

 

Ya kara da cewa, fitar da sakamakon na cikin 2025 na SSCE cikin sauki, shaida ne na ma’aikatan Hukumar Jarrabawar bisa kwarewa, da’a da kuma ci gaba da neman nagartarsu, da sanin ya kamata, da kula da inganci, da jajircewa wajen bin ka’idojin da’a, sun tabbatar da cewa NECO ta samar da sakamakon da ya dace kuma dalibai, cibiyoyi da sauran jama’a suka amince da su.

 

 

Farfesa Dantani ya bayyana matukar godiya ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinuba bisa jajircewarsa wajen ganin an inganta ilimi ya samar da kyakkyawan yanayi ga hukumar NECO ta samu ci gaba, ya kuma yabawa ministan ilimi Dr Maruf Tunji Alyssa da karamin ministan ilimi Farfesa Suwaiba Said Ahmad bisa goyon baya da fahimtarsu.

 

COV ALIYU LAWAL.

 

Labarai

Labarai3 days ago

Matasan Kauru Sun Yi Allah-wadai da Mulkin Ƙarfi, Sun Buƙaci Adalci da Haɗin Kai

  Daga Yusuf Zubairu Wata ƙungiyar matasa a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa shugabanci na bai-ɗaya...

Labarai3 days ago

Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Usman Muhammad Zaria  Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula...

Labarai1 week ago

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida...

Labarai2 weeks ago

Ƙaruwa a Shan Abubuwan Sha Masu Ƙara Ƙarfi na Haddasa Damuwar Lafiya a Kano

Abubuwan sha masu ƙara ƙarfi, waɗanda aka fi sani da energy drinks ko energizers, na ƙara samun karɓuwa a faɗin...

Labarai2 weeks ago

Shugaba Tinubu Ya Taya CPSO Usman Shugaba Murnar Cika Shekara 45 da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Kwamishinan ‘Yan Sanda, Usman Musa Shugaba, wanda shi ne Babban Jami’in Tsaron ‘Yan...

Labarai2 weeks ago

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu...

Labarai2 weeks ago

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru. Malam Suleiman Lawal, mai shekaru...

Labarai2 weeks ago

Gwamnatin Kano Ta Faɗaɗa Damar Tattalin Arziki ga Mata da Masu Buƙata Ta Musamman

An kammala kasuwar baje kolin mata ta tsawon kwanaki huɗu, wadda Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Masu Buƙata Ta Musamman...

Labarai2 weeks ago

Rundunar Tsaro Ta Haɗin Gwiwa Ta Hallaka ’Yan Bindiga 150

Rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ta ƙunshi Sojojin Nijeriya, Hukumar Tsaron Farin Ciki (DSS), ’Yan Sanda da sauran hukumomin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Neja Ta Amince da Sake Buɗe Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu daga 12 ga Janairu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya amince da sake buɗe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin...

Mafi Shahara