Connect with us

Labarai

Jam’iyyar APC ta Zabi Sabbin Shugabanninta a Jihar Zamfara

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Jam’iyyar APC ta gudanar da tarukan zaɓen shugabanni na mazabu da na ƙananan hukumomi cikin nasara a dukkan mazabu 147 da ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara, inda aka fitar da shugabannin jam’iyyar ta hanyar sulhu.

An gudanar da tarukan cikin kwanciyar hankali, kuma an bayyana su a matsayin masu tsari da nagarta, tare da halartar masu ruwa da tsaki da mambobin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar.

Da yake zantawa da manema labarai a Gusau, shugaban kwamitin gudanar da tarukan, Babande Babakura Imam, ya ce an gudanar da aikin cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.

Imam ya bayyana cewa tarukan na mazabu da ƙananan hukumomi sun samu halartar jama’a da yawa, inda aka sami dukkan shugabanni  ta hanyar  sulhu da amincewar mambobin jam’iyyar.

Ya ce, “Jami’an HukumarZabe mai Zaman Kanta ta kasa(INEC), da jami’an tsaro, da wakilan jam’iyyar APC daga sakatariyar ƙasa da ke Abuja, da kuma wakilan APC na jiha ne suka sanya ido kan yadda aka gudanar da tarukan.”

A cewarsa, tarukan ƙananan hukumomi sun fitar da shugabannin APC a dukkan ƙananan hukumomi 14, ciki har da shugabanni, sakatarori da sauran jami’ai.

Shi ma da yake jawabi, shugaban APC na Jihar Zamfara, Alhaji Tukur Danfulani, ya bayyana nasarar gudanar da tarukan a matsayin abin farin ciki ga jam’iyyar.

Danfulani ya yabawa kwamitin tarukan bisa bin ƙa’idojin jam’iyyar yadda ya kamata, wajen gudanar da aikin a duk faɗin jihar, yana mai jaddada cewa APC na da ƙudurin tabbatar da gaskiya da haɗin kai.

Shugaban jam’iyyar ya kuma nuna kwarin gwiwa cewa APC na da haɗin kai gabanin zaɓuka masu zuwa a jihar, yana mai cewa fitowar sabbin shugabanni zai ƙara ƙarfafa tsarin jam’iyyar.

Wannan ci gaba alama ce cewa APC ta shirya tsaf domin ƙwato jihar Zamfara tare da yin aiki domin sake zaɓen Bola Ahmed Tinubu da dukkan ‘yan takarar APC a zaɓen shekarar 2027,” in ji Danfulani.

Ya kuma bayyana gamsuwarsa da yadda mambobin jam’iyyar suka halarci tarukan da kuma yadda aka gudanar da su cikin tsari da lumana a faɗin jihar.

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara