Ilimi
Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
Daga Aminu Dalhatu
Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa Cibiyar Bincike da Adana Tarihi da Al’adun Jihar Zamfara.
Farfesa Adamu ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci tawagar shugabannin jami’ar ziyarar girmamawa ga Sarkin Anka kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad.
Sanarwar da Babban Jami’in Hulɗa da Jama’a na jami’ar, Jamilu Ibrahim Gusau, ya fitar ta ce ziyarar na daga cikin jerin ganawa da masu ruwa da tsaki da Shugaban jami’ar ke yi domin shimfiɗa alkiblar tafiyar da sabuwar gwamnatinsa.

A cewar Farfesa Adamu, cibiyar da ake shirin kafawa za ta mayar da hankali ne kan karewa, tattarawa da bunƙasa tarihin arziki da al’adun gargajiya na Jihar Zamfara.
Ya jaddada cewa wannan shiri na nuna muhimmancin da ake bai wa masarautu da kuma bukatar kare ilimin gargajiya domin amfanin al’umma masu zuwa.

Shugaban jami’ar ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta yi aiki kafada da kafada da Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara domin tabbatar da cewa al’ummar jihar sun amfana da damar ilimi da ci gaba a FUGUS.
Ya yi kira ga Majalisar Sarakunan da ta jagoranci ƙoƙarin ƙara yawan ɗalibai ‘yan asalin Zamfara da ke samun gurbin karatu a jami’ar, yana mai cewa faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi zai taimaka wajen hanzarta ci gaban jihar baki ɗaya.

A nasa jawabin, Sarkin Anka, Alhaji Attahiru Ahmad, ya yaba wa Shugaban jami’ar da tawagarsa kan ziyarar, inda ya bayyana ta a matsayin farkon sabunta haɗin gwiwa tsakanin jami’ar da masarautu.
Ya ce ƙarfafa haɗin kai zai taimaka matuƙa wajen magance ƙalubalen zamantakewa da na ci gaba a jihar.

Sarkin ya kuma bayyana cewa Majalisar Sarakunan Jihar za ta yi aiki tare da jami’ar wajen shirya taruka da bitoci ga sarakunan gargajiya, tare da habbaka gudummawar da masu sarauta ke takawa a faɗin Jihar Zamfara.
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai7 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci7 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
