Connect with us

Labarai

Rundunar ‘Yansandan Kabi Ta Tabbatar da Mutuwar Mutane 33 Sakamakon Fashi da Makami

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi ta ƙara tsaurara matakan tsaro a Gundumar Bui da ke Ƙaramar Hukumar Arewa, bayan wani hari na satar shanu da ya auku a ranar Larabar da ta gabata.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Bashir Usman, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

Sanarwar ta ce an tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki na musamman zuwa yankin, yayin da ake ci gaba da sintiri domin tabbatar da zaman lafiya. Rundunar ta nuna alhini matuƙa kan mutuwar mutane 33 marasa laifi, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan da daukacin al’ummar Arewa.

Binciken farko ya nuna cewa wasu ‘yan bindiga da ake kira Lakurawa ne suka shiga yankin domin satar shanu, kuma ana zargin sun tsallaka ne daga Ƙaramar Hukumar Gudu ta Jihar Sokoto.

Mutanen da abin ya shafa sun fito ne daga garuruwan Mamunu, Awasaka, Tungan Tsoho, Makangara, Kanzo, Gorun Naidal da Dan Mai Ago, inda suka yi yunƙurin mayar da martani, wanda a yayin haka ne aka yi mummunar arangama da ta yi sanadin asarar rayuka.

Rundunar ta jaddada cewa duk wani lamari da ya shafi ‘yan ta’adda masu makami na buƙatar haɗin kai da hukumomin tsaro. Don haka ta buƙaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi mai tayar da hankali ta hanyoyin tsaro da aka tanada, maimakon su ɗauki mataki da kansu, domin irin waɗannan arangama na da matuƙar haɗari.

Ta kuma bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan musamman domin kamo waɗanda suka aikata laifin, hana sake aukuwar irin haka, da kuma ƙarfafa hanyoyin samar da bayanan gaggawa.

Rundunar ta bayar da lambobin wayar ɗakin kula da bayanai kamar haka: 08038797644 da 09015888578 domin kai rahoto cikin gaggawa.

REL SANI DUTSINMA

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci7 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara