Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Published

on

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da mukamin wajen fa’ida ta kansa, da cin amanar jama’a.

Wannan mataki ya biyo bayan korafi da aka mika ga Majalisar daga Shugaban Gwamnati, inda aka bukaci majalisar ta dauki mataki kan Mataimakin Gwamnan saboda zargin rashin da’a a lokacin da yake kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi tsakanin shekarar 2023 zuwa 2024.

Jagoran masu rijaye a majalisar Lawan Hussaini Dala, ya ce sanarwar tsigewar ta dace da Sashe na 188 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya (1999, da aka gyara).

A cewarsa, sanarwar ta nuna cewa Abdulsalam ya aikata abubuwan da ke iya janyo tsige shi yayin da yake kula da kananan hukumomi 44 na jihar.

Zargin da korafin ya kunsa sun hada da: Cin amanar jama’a da Juyar da kudade da Yin amfani da mukami ba bisa ka’ida ba da kuma Rashin da’a da manyan laifuka

An ce:“Abdulsalam ya yi amfani da kudaden da aka ware domin kananan hukumomi domin amfanin kansa. Daga Yuni 2023 zuwa Janairu 2024, an ce ya karɓi ₦462 miliyan a matsayin ribar da aka biya shi. Daga Fabrairu 2024 zuwa Yuli 2024, an ce ya karɓi ₦726 miliyan daga kananan hukumomi ta hanyar aikin musamman.”

Haka kuma, an ce Abdulsalam ya ba da damar sakin ₦440 miliyan ga kamfanin North Med Pharmaceutical Limited ba bisa ka’ida ba, wanda ya saba dokokin sayen kaya na gwamnati da tsarin kasafin kudin jihar.

Dala ya bayyana cewa: “Wadannan ayyuka suna cikin manyan laifuka a ƙarƙashin Sashe 188(2) na Kundin Tsarin Mulki, kuma suna nuna karya ka’idojin mulki da dabi’un shugabanci.”

Dala ya kara da cewa, bisa ga hujjojin da aka gabatar, Abdulsalam ya kamata a korar sa daga mukami bisa tsarin doka.

Rahoton Radio Nigeria ya nuna cewa an bai wa Mataimakin Gwamnan makonni biyu domin ya mayar da martani kan zargin da ke cikin korafin.

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai3 days ago

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro

Ƙungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka SAPPEF a ƙaramar hukumar Lere ta Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar sabon injin motar...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Nasarawa ta Nada Sabon Osu Ajiri na Masarautar Udege

Daga Aliyu Muraki  Gwamnatin Jihar Nasarawa ta amince da nadin Suleiman Ahmed Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na masarautar...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Zamfara Za Ta Gina Dakunan Kwanan Dalibai a Jami’ar Talata Mafara

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta sanar da shirin gina dakunan kwanan dalibai da kuma samar da motocin sufuri...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD

Daga Usman Muhammad Zaria Minista a Ma’aikatar Ayyuka, Barrista Bello Muhammad Goronyo, ya yi alkawarin shiga tsakani wajen samar da...

Labarai6 days ago

‘Yan Sanda Sun Cafke ‘Yan Bindiga Da Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara ta ce ta samu nasarori a ƙoƙarinta na yaƙi da ta’addanci, inda ta ceto...

Labarai6 days ago

Tinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce tsofaffin dokokin haraji na zamanin mulkin mallaka sun talauta ‘yan Najeriya, yana mai...

Labarai6 days ago

NSCDC Ta Gargadi Masu Laifi Da Barayin Kadarori A Kwara

Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kwara ta gargadi masu aikata laifuka da masu lalata kadarorin gwamnati da su kauce...

Labarai6 days ago

Harin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe

Daga Bello Wakili  Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa iyalan jami’an tsaro da aka kashe a wani harin baya-bayan nan da...

Labarai6 days ago

Kashim Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Kebbi

Daga Sani Dutsinma Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnatin tarayya zuwa Jihar Kebbi domin yin...

Kasuwanci6 days ago

Majalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni

Daga Aliyu Lawal  Majalisar Dokokin Jihar Neja ta amince da kudirin dokar daidaita ayyukan Baban bola da masu kasuwancin karafa...

Mafi Shahara