Labarai
Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da mukamin wajen fa’ida ta kansa, da cin amanar jama’a.
Wannan mataki ya biyo bayan korafi da aka mika ga Majalisar daga Shugaban Gwamnati, inda aka bukaci majalisar ta dauki mataki kan Mataimakin Gwamnan saboda zargin rashin da’a a lokacin da yake kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi tsakanin shekarar 2023 zuwa 2024.
Jagoran masu rijaye a majalisar Lawan Hussaini Dala, ya ce sanarwar tsigewar ta dace da Sashe na 188 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya (1999, da aka gyara).
A cewarsa, sanarwar ta nuna cewa Abdulsalam ya aikata abubuwan da ke iya janyo tsige shi yayin da yake kula da kananan hukumomi 44 na jihar.
Zargin da korafin ya kunsa sun hada da: Cin amanar jama’a da Juyar da kudade da Yin amfani da mukami ba bisa ka’ida ba da kuma Rashin da’a da manyan laifuka
An ce:“Abdulsalam ya yi amfani da kudaden da aka ware domin kananan hukumomi domin amfanin kansa. Daga Yuni 2023 zuwa Janairu 2024, an ce ya karɓi ₦462 miliyan a matsayin ribar da aka biya shi. Daga Fabrairu 2024 zuwa Yuli 2024, an ce ya karɓi ₦726 miliyan daga kananan hukumomi ta hanyar aikin musamman.”
Haka kuma, an ce Abdulsalam ya ba da damar sakin ₦440 miliyan ga kamfanin North Med Pharmaceutical Limited ba bisa ka’ida ba, wanda ya saba dokokin sayen kaya na gwamnati da tsarin kasafin kudin jihar.
Dala ya bayyana cewa: “Wadannan ayyuka suna cikin manyan laifuka a ƙarƙashin Sashe 188(2) na Kundin Tsarin Mulki, kuma suna nuna karya ka’idojin mulki da dabi’un shugabanci.”
Dala ya kara da cewa, bisa ga hujjojin da aka gabatar, Abdulsalam ya kamata a korar sa daga mukami bisa tsarin doka.
Rahoton Radio Nigeria ya nuna cewa an bai wa Mataimakin Gwamnan makonni biyu domin ya mayar da martani kan zargin da ke cikin korafin.
Khadijah Aliyu
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Inganta Hanyoyi, Ruwa da Wutar Lantarki a Jami’ar FUD
-
Ilimi7 days agoZamfara Ta Amince Da Shirin Gaggawa Na Kwana 120 Domin Farfaɗo Da Ilimi
-
Labarai6 days agoTinubu: Sabbin Dokokin Haraji Za Su Kawo Wadata Yayinda Tsofaffi Suka Talauta ‘Yan Najeriya
-
Labarai7 days agoHezbollah Da Isra’ila Za Su Yi Ganawar Gaba Da Gaba A Karon Farko
-
Labarai3 days agoƘungiyar Ci gaban Al’ummar Saminaka Ta Bai Wa ‘Yan Sanda Injin Hilux Don Ƙarfafa Tsaro
-
Labarai6 days agoAn Yi wa Yara Sama da 66,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Tarauni
-
Kasuwanci6 days agoMajalisar Neja ta Amince da Dokar Hana Ayyukan Baban Bola a Unguwanni
-
Labarai6 days agoHarin Shanga: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafawa Iyalan Jama’an Tsaro da Aka Kashe
