Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin 2026 a Gaban Majalisa

Published

on

Daga Bello Wakili

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kuɗin shekarar 2026 da ya kai Naira Tiriliyan 58.18 ga zaman haɗin gwiwa na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, inda ya bayyana shi a matsayin “Kasafin Ƙarfafa Ci gaba, Sabunta Juriya da Wadata ga Kowa.”

Da yake jawabi ga ’yan majalisa a Abuja, Shugaban ya ce Dokar Kasafin Kuɗi ta 2026 ta ginu ne bisa sauye-sauyen tattalin arziki da aka aiwatar cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata, waɗanda suka mayar da hankali kan daidaita tattalin arziƙin ƙasa, karfafa masu zuba jari, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai amfani ga kowa.

Shugaba Tinubu ya tsara kashe naira tiriliyan 15.25 domin gudanar ayyukan yau da kullum na gwamnati, sannan ya ware naira tiriliyan 26.08 domin gudanar da manyan ayyuka da more rayuwa a ƙasar.

Tinubu ya tsara kasafin ne a bisa hasashen farashin gangar ɗanyen man fetur a kan dala 64.85.

Haka an yi hasashen sama da gangar ɗanyen man fetur miliyan 1.84 a kullum, sannan ya ayyana canjin dala a kan naira 1,400.

Ma’aikatun da suka fi samun kasafi su ne Ma’aikatar Tsaro, inda za ta sami Naira tiriliyan 5.41, sai ababen more rayu, inda za a kashe Naira tiriliyan 3.56, yayin da Ma’aikatar Ilimi za ta kaishe Naira Tiriliyan 3.52, sai Ma’aikatar Lafiya kuma za ta kashe  Naira tiriliyan 2.48.

Tinubu ya ce tsaro shi ne ginshiƙin ci gaba, inda ya sanar da sake fasalin tsarin tsaron ƙasa da kuma sabon tsarin yaƙi da ta’addanci.

A fannin ilimi kuwa, Shugaban ya bayyana faɗaɗa Shirin Lamunin Ilimi na Ƙasa (NELFUND), wanda ya tallafa wa sama da dalibai 788,000 a manyan makarantu 229.

Yayin gabatar da Dokar Kasafin Kuɗi, Tinubu ya nemi haɗin kai tsakanin ɓangaren zartarwa da majalisa, yana mai cewa “Da haɗin kai da jajircewar al’ummar Najeriya, za mu cika dukkan alkawarin Ajandar Sabunta kudurori (Renewed Hope Agenda),” in ji shi.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara