Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin 2026 a Gaban Majalisa
Daga Bello Wakili
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kuɗin shekarar 2026 da ya kai Naira Tiriliyan 58.18 ga zaman haɗin gwiwa na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, inda ya bayyana shi a matsayin “Kasafin Ƙarfafa Ci gaba, Sabunta Juriya da Wadata ga Kowa.”
Da yake jawabi ga ’yan majalisa a Abuja, Shugaban ya ce Dokar Kasafin Kuɗi ta 2026 ta ginu ne bisa sauye-sauyen tattalin arziki da aka aiwatar cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata, waɗanda suka mayar da hankali kan daidaita tattalin arziƙin ƙasa, karfafa masu zuba jari, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai amfani ga kowa.
Shugaba Tinubu ya tsara kashe naira tiriliyan 15.25 domin gudanar ayyukan yau da kullum na gwamnati, sannan ya ware naira tiriliyan 26.08 domin gudanar da manyan ayyuka da more rayuwa a ƙasar.
Tinubu ya tsara kasafin ne a bisa hasashen farashin gangar ɗanyen man fetur a kan dala 64.85.
Haka an yi hasashen sama da gangar ɗanyen man fetur miliyan 1.84 a kullum, sannan ya ayyana canjin dala a kan naira 1,400.
Ma’aikatun da suka fi samun kasafi su ne Ma’aikatar Tsaro, inda za ta sami Naira tiriliyan 5.41, sai ababen more rayu, inda za a kashe Naira tiriliyan 3.56, yayin da Ma’aikatar Ilimi za ta kaishe Naira Tiriliyan 3.52, sai Ma’aikatar Lafiya kuma za ta kashe Naira tiriliyan 2.48.
Tinubu ya ce tsaro shi ne ginshiƙin ci gaba, inda ya sanar da sake fasalin tsarin tsaron ƙasa da kuma sabon tsarin yaƙi da ta’addanci.
A fannin ilimi kuwa, Shugaban ya bayyana faɗaɗa Shirin Lamunin Ilimi na Ƙasa (NELFUND), wanda ya tallafa wa sama da dalibai 788,000 a manyan makarantu 229.
Yayin gabatar da Dokar Kasafin Kuɗi, Tinubu ya nemi haɗin kai tsakanin ɓangaren zartarwa da majalisa, yana mai cewa “Da haɗin kai da jajircewar al’ummar Najeriya, za mu cika dukkan alkawarin Ajandar Sabunta kudurori (Renewed Hope Agenda),” in ji shi.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
