Connect with us

Labarai

NSCDC Ta Tura Jami’ai Sama da 2000 Kananan Hukumomin Jihar Kaduna Gabanin Bukukuwan Kirsimeti

Published

on

Daga Usman Sani

Kwamandan Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Civil Defence (NSCDC) a Jihar Kaduna, Panam Musa Buba, ya bayar da umarnin tura jami’an tsaro a dukkan kananan hukumomi ashirin da uku na jihar.

A wannan karo, ya umurci a tura jami’ai dubu biyu da ɗari (2,100) domin tabbatar da tsaron al’umma a lokacin bukukuwan ƙarshen shekara.

Wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar jihar, SC Habeeb Badamasi, ya fitar, ta bayyana cewa an daukin matakin hakan ne da nufin ƙarfafa tsaro kafin Kirsimeti, da lokacin Kirsimetin da bayan bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.

Kwamandan Panam Musa Buba ya tabbatar wa mazauna jihar cewa za su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum cikin kwanciyar hankali, inda ya jaddada ƙudurin rundunar wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a tsawon lokacin bukukuwan.

Mun zo ne domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro, domin kowa ya more wannan lokaci na bukukuwa cikin natsuwa,” In ji shi.

Haka kuma, ya gargaɗi masu aikata laifuka da su janye daga duk wani shiri na aikata laifi, yana mai bayyana cewa jami’an NSCDC tare da sauran hukumomin tsaro za su kasance a wurare masu muhimmanci domin hana aikata laifuka.

Jami’anmu sun shirya tsaf, a don haka, duk wanda ya zabi aikata laifi zai fuskanci hukunci mai tsauri,” in ji Kwamandan.

Kwamandan Panam Buba ya kuma bukaci al’ummar Kirista da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwa wajen tunani da nazari kan ainihin ma’anar Kirsimeti.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara