Labarai
Ku Kyale Kananan Hukumomi Su Ci Gashin Kansu- Shugaba Tinubu
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya gargadi gwamnonin jihohi da su guji saba hukuncin Kotun Koli da ya bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu game da kuɗadensu, yana mai gargaɗin cewa ci gaba da rashin bin hukuncin na iya jawo Gwamnatin Tarayya ta shiga tsakani.
Ya jaddada cewa dole ne a mutunta hukuncin tare da aiwatar da shi gaba ɗaya domin ƙarfafa shugabanci a matakin ƙananan hukumomi.
Shugaban ya bayar da wannan gargaɗi ne a yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) karo na 15 na jam’iyyar APC, wanda aka gudanar a Cibiyar Taro ta Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Tinubu ya nuna damuwa kan yadda wasu gwamnatocin jihohi ke ci gaba da riƙe kuɗaɗen rabon da doka ta tanada da ya kamata a bai wa ƙananan hukumomi.
Ya bayyana cewa duk da ya zaɓi nuna haƙuri da girmamawa wajen mu’amala da gwamnonin, Gwamnatin Tarayya na da ikon tilasta bin doka.
Ya yi gargaɗin cewa idan gwamnonin suka ƙi bin hukuncin, Gwamnatin Tarayya na iya fara biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga Asusun Tarayya (Federation Account), bisa tanadin kundin tsarin mulki da kuma umarnin Kotun Koli.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
