Labarai
Kashim Shettima Ya Bayyana Goyon Bayansa Ga Shugaba Tinubu Gabanin Zaben 2027
Daga Bello Wakili
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cikakken kwarin gwiwa ga jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Ya bayyana hakan ne a taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Abuja.
Shettima ya bayyana cewa duk wanda ke ƙalubalantar Shugaban Ƙasa, zaɓi ne na siyasa da mutum ya ɗaukar ma kansa, wanda a karshe zai kai shi ga cizon yatsa.
Ya jaddada cewa duk da cewa Najeriya ƙasa ce ta dimokiraɗiyya inda kowa ke da ’yancin tsayawa takara, tarihin ayyuka da gogewar Tinubu sun sanya shi kaiwa ga wani babban matsayi da ya kamata a jinjina masa.
Shettima ya kuma lura da cewa nasarar zaɓe ta wuce shahara a yanar gizo kawai, yana mai jaddada cewa ba a cin zaɓe ta hanyar hulɗa da kafafen sada zumunta ko hayaniyar jama’a kaɗai.
Ya nuna muhimmancin haɗin kan jama’a, bin gaskiya da sadaukarwa, yana mai cewa irin waɗannan abubuwa ne ke tabbatar da nasara a rumfunan zaɓe, ba fafutuka ko shashi fadi a yanar gizo ba,
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
