Connect with us

Labarai

Kashim Shettima Ya Bayyana Goyon Bayansa Ga Shugaba Tinubu Gabanin Zaben 2027

Published

on

Daga Bello Wakili 

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cikakken kwarin gwiwa ga jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

Ya bayyana hakan ne a taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Abuja.

Shettima ya bayyana cewa duk wanda ke ƙalubalantar Shugaban Ƙasa, zaɓi ne na siyasa da mutum ya ɗaukar ma kansa, wanda a karshe zai kai shi ga cizon yatsa.

Ya jaddada cewa duk da cewa Najeriya ƙasa ce ta dimokiraɗiyya inda kowa ke da ’yancin tsayawa takara, tarihin ayyuka da gogewar Tinubu sun sanya shi kaiwa ga wani babban matsayi da ya kamata a jinjina masa.

Shettima ya kuma lura da cewa nasarar zaɓe ta wuce shahara a yanar gizo kawai, yana mai jaddada cewa ba a cin zaɓe ta hanyar hulɗa da kafafen sada zumunta ko hayaniyar jama’a kaɗai.

Ya nuna muhimmancin haɗin kan jama’a, bin gaskiya da sadaukarwa, yana mai cewa irin waɗannan abubuwa ne ke tabbatar da nasara a rumfunan zaɓe, ba fafutuka ko shashi fadi a yanar gizo ba,

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara