Labarai
Shugaba Tinubu Ya Amince da Sake Kafa Kwamitin Hukumar Kula da Wutar Lantarki
Daga Bello Wakili
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake kafa Kwamitin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da mambobin kwamitin a ranar 16 ga Disamba.
Mambobin sabon kwamitin sun haɗa da: Mulisiu Olalekan Oseni a matsayin Shugaba, da Yusuf Ali a matsayin Mataimakin Shugaba.
Sauran mambobin sun hada da Mista Nathan Rogers Shatti Kwamishina, Mista Dafe Akpeneye Kwamishina, Aisha Mahmud Kanti Bello Kwamishina, Dokta Chidi Ike Kwamishina, da Dokta Fouad Animashaun Kwamishina.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga mambobin kwamitin NERC da su zurfafa tare da ƙarfafa sauye-sauyen da ake yi a ɓangaren wutar lantarki na Nijeriya, bisa bin doka da dokar Wutar Lantarki ta 2023.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
