Connect with us

Labarai

Ma’aikatan Lafiya na BKD-HEALTH Sun Karrama Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Ma’aikatan lafiya na BKD-HEALTH sun karrama shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, bisa shugabanci nagari da kuma daukar matasa aiki.

A jawabinsa na maraba, jagoran ma’aikatan na BKD-HEALTH Nasiru Sanusi ya ce taron ya dace da cikar su shekara daya da samun wannan aiki wanda ma’aikata 210 ke samun alawus ba tare da yankewa ba.

A sakonsa na fatan alkairi, shugaban sashen kula da tsaftar ruwa da muhalli na karamar hukumar ta bakin Malam Saminu Musa, ya ce baya ga daukar ma’aikatan BKD-HEALTH domin inganta aikin lafiya, shugaban karamar hukumar yana kashe naira milyan 5 duk wata wajen tallafawa marasa lafiya da kudaden magani.

Shi ma a nasa jawabin, Kansilan ayyuka Alhaji Haladu Maigari, ya ce cikin watanni da kama mulkinsa, shugaban karamar hukumar ya gyara asibitoci guda 7.

Ya kuma jinjinawa ma’aikatan na BKD-HEALTH bisa lura da kokarin shugaban karamar hukumar, inda ya yi addu’ar nan gaba za a ba su aiki na dindindin.

Wasu daga cikin ma’aikatan na BKD-HEALTH Sulaiman Yusuf, Ai’sha Isma’il Sulaiman da Ummu Salma Abdullahi sun ce sun kwashe shekara da shekaru a matakin aikin sa kai da na wucin gadi.

 

Sun kuma godewa shugaban karamar hukumar bisa samun wannan dama.

Da ya ke mayar da jawabi, shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba ya bukaci ma’aikatan na BKD-HEALTH da su rike ayyukan su bisa gaskiya da Amana domin kuwa karin alawus din su zai dogara akan kwazo da mutunta aiki.

Ya bayyana taron a matsayin cikakkiyar sheda kan abubuwan da ke wakana a karamar hukumar Birnin Kudu.

Builder, ya yi kira ga jama’ar yankin da su shiga a dama da su wajen yankar katin zabe da na jam’iyar APC domin ciban yankin.

Sauran wadanda aka karrama tare da shugaban karamar hukumar sun hadar da Alhaji Haladu Maigari da Alhaji Ibrahim Isyaku da Malam Muhammad Musa Badamasi da Mai kula da shirin BKD-HEALTH, Mujittafa Ibrahim.

 

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara