Labarai
Ma’aikatan Lafiya na BKD-HEALTH Sun Karrama Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
Daga Usman Muhammad Zaria
Ma’aikatan lafiya na BKD-HEALTH sun karrama shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, bisa shugabanci nagari da kuma daukar matasa aiki.
A jawabinsa na maraba, jagoran ma’aikatan na BKD-HEALTH Nasiru Sanusi ya ce taron ya dace da cikar su shekara daya da samun wannan aiki wanda ma’aikata 210 ke samun alawus ba tare da yankewa ba.

A sakonsa na fatan alkairi, shugaban sashen kula da tsaftar ruwa da muhalli na karamar hukumar ta bakin Malam Saminu Musa, ya ce baya ga daukar ma’aikatan BKD-HEALTH domin inganta aikin lafiya, shugaban karamar hukumar yana kashe naira milyan 5 duk wata wajen tallafawa marasa lafiya da kudaden magani.
Shi ma a nasa jawabin, Kansilan ayyuka Alhaji Haladu Maigari, ya ce cikin watanni da kama mulkinsa, shugaban karamar hukumar ya gyara asibitoci guda 7.

Ya kuma jinjinawa ma’aikatan na BKD-HEALTH bisa lura da kokarin shugaban karamar hukumar, inda ya yi addu’ar nan gaba za a ba su aiki na dindindin.
Wasu daga cikin ma’aikatan na BKD-HEALTH Sulaiman Yusuf, Ai’sha Isma’il Sulaiman da Ummu Salma Abdullahi sun ce sun kwashe shekara da shekaru a matakin aikin sa kai da na wucin gadi.
Sun kuma godewa shugaban karamar hukumar bisa samun wannan dama.
Da ya ke mayar da jawabi, shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba ya bukaci ma’aikatan na BKD-HEALTH da su rike ayyukan su bisa gaskiya da Amana domin kuwa karin alawus din su zai dogara akan kwazo da mutunta aiki.
Ya bayyana taron a matsayin cikakkiyar sheda kan abubuwan da ke wakana a karamar hukumar Birnin Kudu.

Builder, ya yi kira ga jama’ar yankin da su shiga a dama da su wajen yankar katin zabe da na jam’iyar APC domin ciban yankin.
Sauran wadanda aka karrama tare da shugaban karamar hukumar sun hadar da Alhaji Haladu Maigari da Alhaji Ibrahim Isyaku da Malam Muhammad Musa Badamasi da Mai kula da shirin BKD-HEALTH, Mujittafa Ibrahim.
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
