Connect with us

Labarai

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Published

on

Daga Bello Wakili 

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin ya shafa a ƙauyen Ngoshe da ke Karamar Hukumar Gwoza ta Jihar Borno.

Shugaban ƙasar ya yi alhinin rasuwar  mutane da ba su ji ba ba su gani ba, ciki har da jami’an soji, da kuma waɗanda suka rasu sakamakon harbin kuskure yayin da jiragen yaƙi ke kai hari ga ‘yan ta’addan da suka tsere.

Ya bayyana harin na ‘yan ta’addan a matsayin mummunan ta’adi da rashin tausayi ga al’umma marasa ƙarfi, tare da kira ga al’ummar Borno da sauran sassan ƙasar da kada su karaya.

Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa sojojin bisa  martanin gaggawa da suka mayar, wanda ya yi sanadiyyar kashe ‘yan ta’adda da dama tare da tilasta musu janyewa daga yankin.

Ya kuma umarci sojoji da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta  ceto mutanen da ‘yan ta’addan suka sace.

Bugu da ƙari, Shugaban ya umarci rundunar sojoji da ta ƙara ƙaimi wajen kare fararen hula a faɗin ƙasar da kuma hana kai hare-hare kan sansanonin soji musamman a yankin Arewa maso Gabas.

Shugaba Tinubu ya yi addu’ar Allah Ya ji ƙan waɗanda suka rasu a harin da kuma harbin kuskure, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalansu da kuma Gwamnatin Jihar Borno.

Labarai

Labarai3 hours ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai4 hours ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai10 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai10 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai10 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai10 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai10 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai10 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai10 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai10 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara