Connect with us

Ilimi

UNICEF Ta Bukaci a Gaggauta Inganta Ayyukan Ruwa da Tsaftar Muhalli a Makarantu da Asibitocin Kano da Jigawa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Kula da Yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ta yi kira da a dauki matakan gaggawa domin inganta ayyukan ruwa, tsafta da muhalli (WASH) a makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a jihohin Kano da Jigawa.

Babban Jami’in Ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ne ya bayyana hakan yayin taron tattaunawa da kafafen yada labarai da masu ruwa da tsaki kan ayyukan WASH a jihohin biyu.

Farah ya ambato sakamakon binciken WASHNORM II na shekarar 2021, wanda ya nuna cewa kashi 11 cikin 100 ne kacal na makarantu a fadin kasar ke da damar samun muhimman ayyukan ruwa, tsafta da muhalli, yayin da kashi shida cikin 100 kawai na cibiyoyin lafiya ke cika wannan ka’ida.

Ya ce halin ya fi muni a yankunan karkara na Arewa maso Yammacin Najeriya, inda rashin wadatattun kayayyakin WASH ke sa miliyoyin yara kamuwa da cututtukan da za a iya karewa, kamar gudawa da kwalara.

A cewarsa, duk da cewa Jihar Jigawa ta samu ci gaba wajen kokarin zama jihar da ba a yin bahaya a fili, har yanzu kayayyakin wanke hannu da ingantattun gine-ginen tsafta a makarantu na karanci, lamarin da ke barazana ga lafiyar yara da karatunsu.

Mista Rahama Rihood Farah ya jaddada cewa makarantu da cibiyoyin lafiya da ba su da isassun ayyukan WASH na iya zama wuraren yaduwar cututtuka cikin sauri, lamarin da ke haddasa karuwar yawan daliban da ke fashin zuwa makaranta, musamman ‘yan mata.

Ya bayyana cewa munanan yanayin WASH na kawo cikas ga kokarin Najeriya na cimma Muradun Cigaban Mai Dorewa (SDGs) a fannin ilimi da samar da ruwan sha mai tsafta da tsaftar muhalli ga kowa.

Farah ya bayyana cewa tare da goyon bayan masu bayar da tallafi, UNICEF na aiki da gwamnatoci wajen inganta ayyukan WASH, ciki har da kaddamar da cibiyoyin lafiya da ilimi guda 84 masu jure sauyin yanayi a Kano da Jigawa, karkashin shirin CRIBS na fam miliyan 19 da Birtaniya ta dauki nauyi.

Ya kara da cewa an fadada shirin zuwa wasu jihohi bayan nasarar da ya samu a jihohin biyu.

Jami’in na UNICEF ya kuma jaddada muhimmancin kula da gyara da kula da kayayyakin WASH yadda ya kamata domin tabbatar da amfanin su na dogon lokaci.

Farah ya bukaci kafafen yada labarai da su taka rawar gani wajen fallasa gibin ayyukan WASH, sa ido kan kashe kudaden jama’a, rike hukumomi da kula da su, da kuma yin kira da a inganta kayayyaki a makarantu da cibiyoyin lafiya.

Ya ce ci gaba da fafutukar kafafen yada labarai na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da lafiyayyen muhallin koyo ga yara a fadin Arewa maso Yammacin Najeriya.

 

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara