Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara ta Bada Babura 10 ga ‘Yan Sanda a Jihar Domin Inganta Tsaro

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayar da sabbin babura guda goma domin ayyukan tsaro ga Ofishin ’Yan Sanda na Gusau ta Tsakiya da nufin ƙarfafa sintiri da inganta tsaro a cikin babban birnin jihar.

An mika baburan ga DPO na ofishin ‘Yan Sanda da ke Gusau ta Tsakiya, CSP Abubakar Sani Muhammad, ta hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada.

Wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai a Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ta bayyana cewa Sakataren Gwamnatin ya samu wakilcin Babban Sakataren Harkokin Majalisar Zartarwa Dakta Abubakar Mohammad Gusau.

Malam Nakwada ya bayyana cewa an bayar da baburan ne domin inganta ayyukan ’yan sanda, musamman a wuraren da ba su da sauƙin shiga da motocin sintiri.

Ya kuma ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa Ofishin ‘Yan Sandan ta hanyar samar da man fetur da za su rika amfani da shi a ababen hawansu domin tabbatar da ingantaccen aiki da dorewar hidimar tsaro.

A cewarsa, wannan tallafi na daga cikin ƙudirin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal na yaƙi da dukkan nau’ikan ayyukan ta’addanci da kuma ƙarfafa tsaro a fadin Jihar Zamfara.

Da yake karɓar Baburan a madadin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya, DPO CSP Abubakar Sani Mohammad ya nuna godiyarsa ga gwamnatin jihar, inda ya ce Baburan za su ƙara wa sashen ƙarfi wajen tinkarar masu aikata laifuka da ke amfani da wurare masu wahalar shiga wajen aikata ayyukan ta’addanci.

Ya yabawa Gwamna Dauda Lawal bisa ci gaba da ba hukumomin tsaro tallafi, tare da tabbatar da kara jaddada cewa za su ci gaba da sauke nauyin da aka dora musu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

A wani labari mai nasaba da hakan, gwamnatin jihar na ci gaba da gyarawa da sake fasalin Ofishin ’Yan Sanda na Gusau ta Tsakiya da kuma Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Zamfara, akan kudi kuɗaɗe kimanin Naira Miliyan 726 da dubu 900 na ofishin Gusau ta Tsakiya, da kuma Naira biliyan 1 da miliyan 400 a hedikwatar.

Labarai

Labarai19 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara