Labarai
Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina
Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin dajin Rugu, wurin da ’yan bindiga ke fakewa a jihohin Katsina da Zamfara.
Daga cikin wadanda aka kashe akwai fitaccen jagoran ’yan bindiga Damale, da kuma Alti, wanda yake mataimaki ga wani jagoran ’yan bindiga mai suna Adamu Alieru.
Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Dakta Mu’azu Danmusa, ya ce jami’an tsaro sun samu sahihan bayanai cewa ’yan bindiga na shirin kai hari kan wata al’umma da ta dakile satar shanu a yankin.
Ya ce lamarin ya fara ne a ranar 5 ga Maris lokacin da ’yan bindiga dauke da makamai suka kai hari kauyen Alhazawa a karamar hukumar Musawa domin satar shanu. Sai dai mazauna yankin tare da wasu ’yan bindiga da suka tuba suka fatattake su, inda aka kashe hudu daga cikinsu kuma aka kwato shanun.
Washegari kuma ’yan bindigar suka dawo da yawa domin daukar fansa, amma suka yi karo da sojoji na sansanin Dan-Ali, inda aka yi artabu har sojojin suka kashe dukkanin ’yan bindigar 45.
Kwamishinan ya yabawa sojoji kan kokarinsu, tare da rokon al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanan sirri domin kare yankunansu.
Isma’il Adamu/Kastina
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai6 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
