Connect with us

Ilimi

UNICEF Ta Jinjinawa Jihohin Kano, Katsina da Jigawa Bisa Inganta Rayuwar Kananan Yara

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ta yaba wa jihohin Kano, Katsina da Jigawa kan manyan ci gaba da suka samu a fannin walwalar yara, tana gargadin cewa har yanzu akwai aikace-aikacen da dama da ya rage a yi.

A yayin ƙaddamar da rahoton Nigerian Child 2025 a Kano, Shugaban Ofishin UNICEF na Kano, Rahama Rihhood Mohammed Farah, ya ce jihohin Kano, Katsina da Jigawa sun samu gagarumin ci gaba a fannonin lafiya, abinci mai gina jiki, ilimi da samar da ruwan sha mai tsafta ta hanyar haɗin gwiwar hukumar da gwamnatocin jihohin.

Daga cikin nasarorin da Farah ya ambata akwai  Masaki Initiative a Jihar Jigawa,  wani shiri da al’umma ke jagoranta wajen yaki da rashin abinci mai gina jiki, inda yanzu sauran jihohi ke koyi da su.

Ya ƙara da cewa Jigawa ta samu babbar nasara a rigakafin cututtuka na yara a cikin shekarun da suka gabata.

A Katsina kuma, UNICEF ta ce gwamnatin jihar ta ware sama da naira biliyan ɗaya domin sayen abincin farfaɗo da yara masu fama da rashin gina jiki (RUTF) ta hanyar Child Nutrition Match Fund.

Ya kuma ce Katsina ta zama jiha ta biyu a Najeriya da ta kai matsayin Open Defecation Free (wato kawar da yin bayan gida a fili).

Sai dai duk da waɗannan nasarori, UNICEF ta ce gibin har yanzu yana da girma domin adadin yara masu fama da rashin abinci mai gina jiki ya wuce kashi 50 cikin ɗari a kowace daga cikin jihohin uku, tare da miliyoyin yara da har yanzu ba sa zuwa makaranta.

A don haka Farah ya yi kira a ƙara haɗin kai domin cike waɗannan gibuna.

 

 

 

 

 

Labarai

Labarai3 hours ago

NHIA Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Usman Muhammad Zaria  Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na...

Labarai7 days ago

Baragurbi a Aikin Jarida na Barazana ga Sahihancin Kafafen Yada Labarai – Shugaban NUJ-FRCN

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen FRCN Kaduna, Kwamared Umar Adamu Sarkinfada, ya bayyana cewa mummunan aikin jarida...

Labarai2 weeks ago

Ƙaruwa a Shan Abubuwan Sha Masu Ƙara Ƙarfi na Haddasa Damuwar Lafiya a Kano

Abubuwan sha masu ƙara ƙarfi, waɗanda aka fi sani da energy drinks ko energizers, na ƙara samun karɓuwa a faɗin...

Labarai2 weeks ago

Shugaba Tinubu Ya Taya CPSO Usman Shugaba Murnar Cika Shekara 45 da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Kwamishinan ‘Yan Sanda, Usman Musa Shugaba, wanda shi ne Babban Jami’in Tsaron ‘Yan...

Labarai2 weeks ago

TSARO: Gwamnan Jihar Neja Ya Nuna Alhini Kan Harin ‘Yan Ta’adda a Al’ummomin Borgu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa kan harin ‘yan ta’adda da aka kai wa wasu...

Labarai2 weeks ago

Allah Ya Jikan Jarman Kauru Da Ke Jihar Kaduna

Mun sami labarin rasuwar tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Malam Suleiman Lawal Jarman Kauru. Malam Suleiman Lawal, mai shekaru...

Labarai2 weeks ago

Gwamnatin Kano Ta Faɗaɗa Damar Tattalin Arziki ga Mata da Masu Buƙata Ta Musamman

An kammala kasuwar baje kolin mata ta tsawon kwanaki huɗu, wadda Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Masu Buƙata Ta Musamman...

Labarai2 weeks ago

Rundunar Tsaro Ta Haɗin Gwiwa Ta Hallaka ’Yan Bindiga 150

Rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ta ƙunshi Sojojin Nijeriya, Hukumar Tsaron Farin Ciki (DSS), ’Yan Sanda da sauran hukumomin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Neja Ta Amince da Sake Buɗe Makarantun Gwamnati da Masu Zaman Kansu daga 12 ga Janairu

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya amince da sake buɗe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin...

Ilimi2 weeks ago

Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin...

Mafi Shahara