Connect with us

Labarai

Jihohin Jigawa, Katsina Da Kano Za Su Kaddamar Da Asusun Wutar Lantarki Mafi Girma A Najeriya

Published

on

Jihohin Jigawa, Katsina da Kano sun amince da hadin gwiwa kan kasuwar wutar lantarki ta jihohi uku, tare da samun kaso a kamfanin Future Energies Africa (FEA), wanda shi ne ke da hannun  jari mafi girma a Kano Electricity Distribution Company (KEDCO).

Kwamishinan wutar lantarki na jihar Jigawa, Injiniya Surajo Musa, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse.

Ya ce gwamnonin jihohin ukun sun cimma wannan matsaya ce a birnin Marrakech, kasar Morocco, yayin taron kolin manyan jami’ai kan samar da wutar lantarki.

Injiniya Surajo Musa ya kara da cewa a yayin taron, jihohin Kano da Katsina sun amince da yin hadin gwiwa da jihar Jigawa wajen samun kaso a Future Energies Africa, domin karfafa tsare-tsaren ci gaban KEDCO.

Jihohin uku tare da kamfanin Future Energies Africa za su kaddamar da wani asusun samar da wutar lantarki na musamman  wanda shi ne irinsa na farko  da ake sa ran zai kai Naira Biliyan 50 a matakin farko, domin hanzarta samar da wuta a cikin jihohin uku,” in ji shi.

Sanarwar ta kara da cewa jihohin za su duba hanyoyin da Dokar Wutar Lantarki (Electricity Act) ta tanada, domin yin hadin gwiwa kan kasuwar wutar lantarki ta jihohin uku, inda kowanne zai amfana.

Ya ce FEA tare da gwamnonin jihohin uku za su rika gudanar da taron kasa da kasa sau daya a shekara, sannan su rika ganawa duk bayan watanni uku domin duba ci gaba da karfafa dangantakar kasuwar wutar lantarki ta Arewa maso Yamma.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara