Connect with us

Labarai

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Published

on

Daga Bello Wakili 

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare ƙasar, tare da tabbatar musu cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da inganta jin daɗinsu da kuma tallafa wa ayyukansu.

Shugaban ya bayar da wannan tabbaci ne yayin wani taron buɗa-baki na mabiya addinin Musulunci da na Kirista da ya yi tare da jami’an Rundunar Sojin ƙasa da sauran hukumomin tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Shugaba Tinubu ya ce taron ya nuna haɗin kan al’ummar Najeriya, yana mai cewa watan Ramadan lokaci ne na yin tunani a kan rayuwa, tsarkake  zuciya da kuma ƙarfafa zaman lafiya tsakanin mabambantan addinai.

Ya yaba wa sojoji kan jajircewarsu wajen kare ƙasa duk da ƙalubalen da suke fuskanta, ciki har da nisantar iyalansu da kuma fuskantar barazanar ‘yan ta’adda da ‘yan Bindiga.

Shugaban ƙasar ya tabbatar musu cewa sadaukarwar da suke yi ba za ta fadi a banza ba, yana mai ƙara cewa jin daɗin sojoji da iyalansu zai ci gaba da kasancewa muhimmin abin da gwamnatinsa za ta bai wa fifiko.

Shugaba Tinubu ya kuma amince da cewa akwai matsalolin ƙarancin gidaje ga sojoji, yana mai cewa gwamnati na aiki tare da sauran masu ruwa da tsaki domin magance matsalar.

Dangane da halin tattalin arzikin ƙasar, shugaban ya bayyana cewa duk da cewa Najeriya ta fuskanci ƙalubale masu tsanani a farkon mulkinsa, matakan da gwamnati ta ɗauka sun fara haifar da Da mai ido.

Ya bayyana kwarin gwiwa cewa ƙasar ta fara fita daga mawuyacin hali na tattalin arziki, tare da bada tabbacin cewa nan gaba kadan za a kara ganin canji mai ma’ana a Najeriya.

Shugaban ƙasar ya kuma miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno kan wani sabon lamari na rashin tsaro da ya faru a jihar, yana mai cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da tallafa wa ƙoƙarin da ake yi domin kawo ƙarshen ta’addanci da ‘yan bindiga a faɗin ƙasar.

Tun da farko, Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya gode wa shugaban ƙasa bisa shirya taron buɗa-bakin na haɗin gwiwar addinai, tare da yaba masa kan amincewa da matakan da nufinsu shi ne inganta jin daɗin jami’an rundunar soji.

Ya kuma yaba wa shugaban ƙasan kan amincewa da ƙarin albashi ga sojoji, ƙarin alawus ga rundunar Brigade of Guards, da kuma amincewa da sayen sabbin kayan aiki da inganta matsugunan sojoji.

Laftanar Janar Shaibu ya ce waɗannan matakai za su taimaka matuƙa wajen ƙara inganta aikin rundunar da kuma ƙarfafa gwiwar jami’anta.

Haka kuma ya sake jaddada biyayyar rundunar sojin ƙasa ga shugaban ƙasa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen kare dimokuraɗiyyar Najeriya da kuma martabar ƙasar.

Labarai

Labarai5 hours ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai6 hours ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai12 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai12 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai12 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai12 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai12 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai12 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai12 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai12 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara