Labarai
Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji
Daga Bello Wakili
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare ƙasar, tare da tabbatar musu cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da inganta jin daɗinsu da kuma tallafa wa ayyukansu.
Shugaban ya bayar da wannan tabbaci ne yayin wani taron buɗa-baki na mabiya addinin Musulunci da na Kirista da ya yi tare da jami’an Rundunar Sojin ƙasa da sauran hukumomin tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Shugaba Tinubu ya ce taron ya nuna haɗin kan al’ummar Najeriya, yana mai cewa watan Ramadan lokaci ne na yin tunani a kan rayuwa, tsarkake zuciya da kuma ƙarfafa zaman lafiya tsakanin mabambantan addinai.
Ya yaba wa sojoji kan jajircewarsu wajen kare ƙasa duk da ƙalubalen da suke fuskanta, ciki har da nisantar iyalansu da kuma fuskantar barazanar ‘yan ta’adda da ‘yan Bindiga.
Shugaban ƙasar ya tabbatar musu cewa sadaukarwar da suke yi ba za ta fadi a banza ba, yana mai ƙara cewa jin daɗin sojoji da iyalansu zai ci gaba da kasancewa muhimmin abin da gwamnatinsa za ta bai wa fifiko.
Shugaba Tinubu ya kuma amince da cewa akwai matsalolin ƙarancin gidaje ga sojoji, yana mai cewa gwamnati na aiki tare da sauran masu ruwa da tsaki domin magance matsalar.
Dangane da halin tattalin arzikin ƙasar, shugaban ya bayyana cewa duk da cewa Najeriya ta fuskanci ƙalubale masu tsanani a farkon mulkinsa, matakan da gwamnati ta ɗauka sun fara haifar da Da mai ido.
Ya bayyana kwarin gwiwa cewa ƙasar ta fara fita daga mawuyacin hali na tattalin arziki, tare da bada tabbacin cewa nan gaba kadan za a kara ganin canji mai ma’ana a Najeriya.
Shugaban ƙasar ya kuma miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno kan wani sabon lamari na rashin tsaro da ya faru a jihar, yana mai cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da tallafa wa ƙoƙarin da ake yi domin kawo ƙarshen ta’addanci da ‘yan bindiga a faɗin ƙasar.
Tun da farko, Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya gode wa shugaban ƙasa bisa shirya taron buɗa-bakin na haɗin gwiwar addinai, tare da yaba masa kan amincewa da matakan da nufinsu shi ne inganta jin daɗin jami’an rundunar soji.
Ya kuma yaba wa shugaban ƙasan kan amincewa da ƙarin albashi ga sojoji, ƙarin alawus ga rundunar Brigade of Guards, da kuma amincewa da sayen sabbin kayan aiki da inganta matsugunan sojoji.
Laftanar Janar Shaibu ya ce waɗannan matakai za su taimaka matuƙa wajen ƙara inganta aikin rundunar da kuma ƙarfafa gwiwar jami’anta.
Haka kuma ya sake jaddada biyayyar rundunar sojin ƙasa ga shugaban ƙasa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen kare dimokuraɗiyyar Najeriya da kuma martabar ƙasar.
-
Labarai6 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai4 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai6 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai5 days agoGwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri
-
Labarai3 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
