Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin shugabannin rikon kwarya na kungiyar ‘yan Achaba na yankin.

A Jawabin da ya gabatar a yayin kaddamarwar a fadar Hakimi, Dr Muhammad Uba yace an nada sabbin shugabanin ne domin samun zaman lafiya a tsakanin su.

Ya kuma hore su da su bi dokoki da ka’idojin kungiya, tare da baiwa Karamar hukumar hadin kai da goyan baya wajen kai rahotan zuwan bakin ‘yan achaba dan tabbatar da tsaro.

Builder Muhammed Uba ya ba su tabbacin samun hadin kai da goyan bayan Karamar hukumar, ya kuma nuna rashin jin dadi da yawan sace sacen babura a yankin.

Kazakika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa kokarin sa na tabbatar da tsaro.

Shi ma a nasa jawabin, Hakimin Birnin Kudu Alhaji Hussaini Hassan jibrin ya bada shawarar yiwa Babura lambobi domin samun saukin ganewa tare da basu horo dan kwarewa akan aikin achaba.

A jawaban su daban daban, Shugaban ‘yan achaba na jihar, Abbas Abdulkadir da sakataren kungiyar, Yau Muhammad sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa daukar matakin nada shugabannin riko na kungiyar ‘yan achaba na yankin.

A jawabin sa na godiya, sabon shugaban rikon kungiyar ‘yan Achaba na yankin Auwalu Ibrahim ya bada tabbacin yin aiki bil hakki da gaskiya.

Labarai

Labarai4 hours ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai5 hours ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai11 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai11 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai11 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai11 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai11 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai11 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai11 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai11 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara