Connect with us

Labarai

Aliko Dangote ya Miƙa Korafi ga Hukumar ICPC Kan Shugaban NMDPRA Farouk Ahmed

Published

on

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya miƙa wa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Nijeriya, ICP ƙorafi kan shugaban Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Nijeriya, NMDPRA,  Ahmed Farouk, kan zarginsa da cin hanci da kuma almubazzaranci da dukiya.

A cikin takardar ƙorafin da aka gabatar a ranar 16 ga Disamba, Dangote ya nemi a kama Ahmed, a gudanar da bincike tare da gurfanar da shi a gaban ƙuliya bisa zarginsa da yin rayuwar ƙarya fiye da ƙarfinsa a matsayin ma’aikacin gwamnati.

A cikin takardar ƙorafin, wadda ofishin Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu (SAN) ya samu, Dangote ya zargi shugaban NMDPRA da kashe fiye da dala miliyan bakwai ba tare da wata shaida ta halastacciyar hanyar samun kuɗaɗen shiga ba, har na tsawon shekaru shida kafin a biya kudin makarantar ‘ya’yansa hudu a makarantu daban-daban a Switzerland.

A cikin takardar ƙorafin, wadda ofishin Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu (SAN) ya samu, Dangote ya zargi shugaban NMDPRA da kashe fiye da dala miliyan bakwai ba tare da wata shaida ta halastacciyar hanyar samun kuɗaɗen shiga ba, har na tsawon shekaru shida kafin a biya kudin makarantar ‘ya’yansa hudu a makarantu daban-daban a Switzerland.

A cikin takardar ƙorafin, Dangote ya ambaci sunayen ‘ya’yan Ahmed guda hudu da makarantunsu da ke Switzerland, ciki har da adadin da aka biya wa kowannensu don tabbatar da zarginsa da kuma neman hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta yi bincike.

Ya yi zargin cewa Ahmed yana amfani da tsarin NMDPRA don wawure da karkatar da kudaden jama’a don amfanin kai da kuma neman wata manufa ta ƙashin-kai don cutar da al’ummar Nijeriya, lamarin da ya jawo bore da ƙungiyoyi daban-daban suka yi kwanan nan.

Dangote ya yi iƙirarin cewa a tsawon rayuwar shugaban NMDPRA a matsayinsa na ma’aikacin gwamnati a Nijeriya duka abin da ya samu ko dala miliyan bakwai bai kai ba.

Ɗan kasuwan ya ce ana zargin an karkatar da kuɗin daga asusun gwamnati don biyan kuɗin karatun ‘ya’yansa a ƙasashen waje.

‘Yin abin da ya dace’

“Babu shakka gaskiyar da ke sama game da cin amanar ofis, karya Dokar Ɗa’a ga jami’an gwamnati, azurta kai daga cin hanci da rashawa, da almubazzaranci babban laifi ne na cin hanci da rashawa wanda Hukumarku (ICPC) ta ba da iko bisa doka a ƙarƙashin sashe na 19, na Dokar ICPC don bincike da gurfanarwa,” in ji Dangote.

“Bayan nasarar gurfanar da irin wannan mutumin, a ƙarƙashin sashe na 19 na Dokar ICPC, mutumin zai fuskanci ɗaurin shekaru biyar ba tare da zaɓin tara ba.

“Muna da ƙarfin hali mu bayyana cewa ICPC tana da matsayi mai kyau tare da hukumomin ‘yan’uwanta don gurfanar da laifukan kuɗi da sauran laifukan da suka shafi cin hanci da rashawa, kuma bayan kafa shari’ar farko, Kotuna ba sa jinkirin hukunta masu laifi.

Dangote ya yi alƙawarin gabatar da hujjoji don tabbatar da zarginsa na wadaƙar da Ahmed ke yi da azurta kansa da cin amanar aikinsa.

‘Yan Nijeriya na buƙatar su san gaskiya’

“Na sha jin mutane da ke korafi game da wani ma’aikacin gwamnati wanda ya sanya ‘ya’yansa a wata makarantar sakandare, inda a cikin shekaru shida aka kashe wa hudu daga cikinsu dala miliyan biyar daga kuɗaɗen Nijeriya,” in ji shi a wani taron manema labarai a Matatar Dangote da ke yankin Ibekku-Lekki na Jihar Legas.

“‘Ya’yana sun je makarantar sakandare a Nijeriya. Ba su je wata ƙasa daban don halartar makarantar sakandare ba.”

A ranar Talata, Dangote ya wallafa cikakkun bayanai game da zarge-zargen a wata jarida kuma bayan awanni kadan ya miƙa takardar ƙorafi kan shugaban NMDPRA.

Shugaban Matatar Dangote ya ce, “‘Yan Nijeriya sun cancanci sanin tushen wadannan kudaden da wani jami’in gwamnati ya biya yayin da iyaye da yawa a jiharsa ta Sokoto ba za su iya biyan kudin makaranta na N10,000 ga ‘ya’yansu da unguwanninsu ba.”

Ya zargi hukumar da kawo cikas ga kokarin inganta matatun man fetur na gida musamman tare da ci gaba da bayar da lasisin shigo da kaya.

Labarai

Labarai6 hours ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai7 hours ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai13 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai13 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai13 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai13 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai13 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai13 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai13 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai13 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara