Ilimi
Gwamna Lawal Ya Nada Sabon Shugaban Jami’ar Jihar Zamfara
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Farfesa Ibrahim Abdullahi Tsafe a matsayin sabon Shugaban Jami’ar Jihar Zamfara da ke Talata Mafara (ZAMSUT), na wa’adin shekara biyar kacal.
Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da wannan naɗin ta hannun Babban Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Sulaiman Ahmad Tudu.
Ya bayyana cewa naɗin ya biyo bayan shawarwarin Majalisar Gudanarwar Jami’ar.
Farfesa Tsafe fitaccen malami ne wanda ya samu digirin Digirgir (PhD) a shekarar 2006, kuma Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto (UDUS) ta ɗaga shi zuwa matsayin Farfesa a shekarar 2013.
Ya rike mukamai daban-daban na gudanarwa, ciki har da zama shugaban Tsangayar Nazarin Halittu da Sinadarai a UDUS. Haka kuma, ya yi aiki a matsayin Visiting Professor a ZAMSUT tun shekarar 2018, kuma a halin yanzu shi ne shugaban tsangayar kimiyya a jami’ar.
Gwamna Lawal ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa Farfesa Tsafe zai yi amfani da ƙwarewarsa da gogewarsa wajen ɗaga darajar Jami’ar ZAMSUT zuwa matsayi mafi girma, bisa manufar gwamnatinsa ta bunƙasa ilimi da nagartar karatu.
-
Ilimi7 days agoFarfesa Gumel Ya Fitar da Sabon Tsari da Zai Daga Martabar FUD
-
Labarai3 days agoHukumar Raya Kogin Benuwe Ta Bullo da Sabuwar Fasahar Kare Hanyar Ban-ruwa a Tafkin Geriyo
-
Ilimi3 days agoAn Gudanar da Liyafar Taya Murna ga Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Dutse
-
Labarai5 days agoGwamnatin Tarayya ta Bada Tallafin Kayayyakin Aiki Gona ga Ƙananan Manoma a Jigawa
-
Labarai6 days agoAn Fara Bikin Kamun Kifi da Al’adu na Ƙasa da Ƙasa na Argungu na Bana
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Amince da Shirin Ciyarwar Watan Ramadan na Bana
-
Labarai6 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Ja Hankalin Maniyyata Game da Muhimmancin Halartar Taron Bita
-
Labarai6 days agoJigawa: Hukumar Alhazai ta Bai wa Amirul Hajji Tabbacin Cikakken Goyon Baya
