Connect with us

Labarai

NUJ Ta Karrama Daraktar Asibitin Kula da Cututtukan Kwakwalwa na Tarayya, Kaduna, da Lambar Yabo

Published

on

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ), Reshen Jihar Kaduna, ta karrama Daraktar Asibitin Kula da Cututtukan Kwakwalwa na Tarayya da ke Kaduna, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u, da Lambar Yabo ta Kyakkyawan Aikin Hidimar Jama’a da Nagarta, sakamakon kyakkyawan jagoranci da gagarumar gudummawar da ta bayar wajen inganta lafiyar jama’a, musamman a fannin kula da lafiyar kwakwalwa.

 

An mika lambar yabon ne a yayin Makon -yan Jarida na Shekara ta 2025 na NUJ Reshen Jihar Kaduna, wanda aka gudanar a ranar Asabar, 13 ga Disamba, 2025, a otel Bafra Ungwan Sarki, Kaduna.

 

An shirya taron ne karkashin taken: “Kafofin Watsa Labarai da Tsarin Zaman Lafiya na Jihar Kaduna: Tattaunawa, Tsaro da Ci gaba a Arewa.”

Yayin gabatar da lambar yabon, NUJ Reshen Jihar Kaduna ta bayyana Farfesa Armiya’u a matsayin fitacciyar jami’ar gwamnati wadda wa’adinta a matsayin Darakta ya kasance cike da nagarta, kwarewa da kuma tsari mai mayar da hankali ga al’umma wajen bayar da ayyukan kiwon lafiya.

 

 

Kungiyar ta jaddada cewa jagorancinta ya karfafa ayyukan kiwon lafiyar jama’a ta hanyar inganta kula da lafiyar kwakwalwa, fadada wayar da kai a cikin al’umma, bunkasa ma’aikata, da kuma ci gaba da fafutukar wayar da kai kan lafiyar kwakwalwa.

 

A cewar NUJ, lambar yabo ta kyakkyawan aikin hidimar jama’a da nagarta tana nuna jajircewar Farfesa Armiya’u wajen jagoranci na gaskiya, rikon amana, da hidima ga bil’adama, musamman wajen daukar lafiyar kwakwalwa a matsayin muhimmin bangare na lafiyar jama’a da ci gaban al’umma.

A jawabinta na godiya, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u ta nuna matukar godiya ga NUJ bisa wannan karramawa, inda ta bayyana lambar yabon a matsayin abin karfafa gwiwa domin ci gaba da nagarta a aikin gwamnati.

 

 

Ta jaddada muhimmiyar rawar da kafofin watsa labarai ke takawa wajen wayar da kan jama’a kan al’amuran kiwon lafiya, bunkasa fahimtar lafiyar kwakwalwa, da kuma tallafa wa manufofin da ke inganta zaman lafiya, tsaro da ci gaba.

 

Ta sadaukar da lambar yabon ga shugabanci da daukacin ma’aikatan Asibitin Kula da Cututtukan Kwakwalwa na Tarayya, Kaduna, tare da yaba musu bisa jajircewa, hadin kai da kwarewa wajen bayar da ayyukan lafiyar kwakwalwa cikin tausayi ga al’umma.

 

Makon Jarida na NUJ na ci gaba da zama muhimmiyar dandali na tattaunawa kan rawar kafofin watsa labarai a harkokin mulki da ci gaba, tare da karrama mutane da hukumomin da suka yi fice wajen hidimar jama’a

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara