Connect with us

Labarai

NLC Ta Gudanar da Gangamin Lumana a Kano

Published

on

Daga Abdullahi Jalaluddeen

Kungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta gudanar da gangamin lumana a jihar Kano domin jawo hankalin jama’a kan ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasa, tare da miƙa wasikar bukatu ga Gwamnatin Jihar Kano.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Kano, Dakta Suleiman Sani Wali, wanda ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin jihar na da kyakkyawar alaka da ƙungiyoyin ƙwadago, inda ya bayyana gangamin a matsayin shaida ta zaman lafiya da fahimta tsakanin gwamnati da ma’aikata.

Ya bayyana gamsuwarsa bisa yadda aka gudanar da gangamin cikin lumana da tsari, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da jajircewa wajen yin mu’amala mai kyau da ƙungiyoyin ƙwadago.

Shugaban Ma’aikatan ya tabbatar wa NLC cewa ana ɗaukar batutuwan tsaro da muhimmanci a jihar, inda ya ce dukkan hukumomin tsaro na aiki gwargwadon ƙarfinsu domin ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a Kano.

Ya kuma ce gwamnan zai duba wasikar da NLC ta gabatar tare da tabbatar da cewa an isar da abubuwan da ke cikinta ga hukumomin da suka dace, ciki har da Shugaban Ƙasa.

Tun da fari, wakilin Shugaban NLC na ƙasa, Mista Muttaqa Yusha’u, ya ce gangamin ya yi daidai da kudurin Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na NLC na shirya gangamin lumana a fadin ƙasar domin wayar da kan jama’a kan matsalar rashin tsaro da kuma inganta zaman lafiya.

Yusha’u ya jaddada cewa rashin tsaro na shafar ma’aikata a kowane fanni, ciki har da malamai, ma’aikatan lafiya, manoma, ’yan kasuwa da jami’an tsaro, yana mai cewa ba za a samu ci gaba ba tare da tsaro da zaman lafiya ba.

Ya yi kira da a samar da tsarin hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da kananan hukumomi, tare da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin ma’aikata, domin shawo kan matsalolin tsaro yadda ya kamata.

Haka nan, Shugaban NLC na Jihar Kano, Mista Kabiru Inuwa, ya yaba wa Gwamnatin Jihar Kano bisa ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a jiharjisai dai ya bukaci a ƙara ƙaimi domin hana yaɗuwar rashin tsaro daga sauran sassan ƙasar.

Inuwa ya jaddada buƙatar inganta walwala da tallafi ga jami’an tsaro da iyalansu, yana mai bayyana cewa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatoci da ƙungiyoyin ƙwadago shi ne hanya mafi dacewa ta samar da tsaro mai ɗorewa.

Kungiyar NLC ta sake jaddada aniyar ta na goyon bayan duk wata gwamnati da ke bada fifiko ga walwalar ma’aikata, zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara