Labarai
’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa
Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki a hanyar Gitata zuwa Gunduma a karamar hukumar Keffi.
Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, SP Ramhan Nansel, ya fitar, ya ce an gano wadanda ake zargin da suna Chigozie Igbokwe da Emmanuel John, dukkansu mazauna Jikwoyi a Abuja.
Sanarwar ta ce an kwato wasu kayayyaki daga hannunsu da suka hada da almakashi na karfe, filaya, mabudai, igiyoyin wuta, da kuma mota kirar Hyundai Sonata mai launin toka mai lambar rajista GWA 44 PM, wadda ake zargin sun yi amfani da ita wajen daukar kayayyakin da suka lalata.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Shatima Jauro Mohammed, ya umarci a mika lamarin zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar a Lafia domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.
Aliyu Muraki/Lafia
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai6 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
