Connect with us

Labarai

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Published

on

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na Musamman Kan Kudi domin tsara tsarin samun kudade mai dorewa ga shirye-shiryen abinci mai gina jiki a fadin Najeriya.

An kafa wannan kwamiti ne a yayin wani taron yanar gizo na Majalisar, inda ake sa ran zai gabatar da taswirar tsarin kudi cikin kwanaki 30 ga NCN da kuma Majalisar Tattalin Arzikin Kasa domin nazari da amincewa.

Kwamiti, wanda Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ke jagoranta, ya kunshi Ministocin Ilimi, Harkokin Ruwa, Harkokin Mata, da Kimiyya da Fasaha, tare da Mataimakin Babban Sakataren Fadar Shugaban Kasa da Babban Mataimakin Musamman kan Lafiya.

Ma’aikatar Kasafi da Shirye-shiryen Tattalin Arziki za ta kasance sakatariya ta wannan kwamitim.

Mataimakin Shugaban Kasa, Shettima, ya jaddada bukatar ajiyar kudade na musamman domin shirye-shiryen abinci da gina jiki, don tabbatar da cewa kudaden da aka ware a kasafin kudi suna haifar da ingantattun canje-canje a rayuwar ‘yan Najeriya.

Ya kuma yi kira da a gaggauta wucewa da Dokar Abinci da Gina Jiki ta Kasa domin samar da tsarin doka da na hukuma mai karfi na hadin kai, samun kudade da kuma alhakin gudanarwa a fadin sassa daban-daban.

Mataimakin Shugaban Kasa ya bukaci Ma’aikatun, Sassa da Hukumomi su tabbatar cewa kudaden da aka amince da su don shirye-shiryen abinci da gina jiki ana sakin su kuma ana amfani da su yadda ya kamata.

Haka kuma, ya karfafa gwamnatocin jihohi su gaggauta aiwatar da shirin domin magance gibin ayyuka a jihohin da ke fama da karancin abinci mai gina jiki.

Bello Wakili

Labarai

Labarai43 minutes ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai1 hour ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai7 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai7 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai7 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai7 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai7 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai7 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai7 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai7 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara