Connect with us

Labarai

Ana Shirin Kaddamar da Sabon Shirin Karatu Kan Cutuka Masu Yaduwa

Published

on

Cibiyar Kasa ta Lafiyar Jama’a da Cututtuka Masu Yaduwa ta bayyana shirin kaddamar da wani sabon shirin karatu domin kara inganta kwarewar ma’aikatan lafiya wajen yaki da cututtuka masu yaduwa.

Babban Daraktan cibiyar, Dakta Abdullahi Aminu Dalhatu, ya bayyana hakan a wajen rufe taron bitar tsara manhajar karatun National Diploma a fannin cututtuka masu yaduwa da alluran rigakafi, da aka gudanar a Zariya.

Ya ce a baya ana koyar da wannan fanni ne a matakan difloma na gaba da kuma kwasa-kwasan takardar shaida, lamarin da ya bar gibi a matakan ma’aikatan lafiya na tsaka-tsaki.

A cewarsa, sabon shirin zai bai wa dalibai ilimi da kwarewar gano cututtuka, hanyoyin kariya da kuma yadda za a kula da su.

Dakta Dalhatu ya kara da cewa cututtuka masu yaduwa na ci gaba da zama babbar barazana ga lafiyar jama’a a Najeriya da sauran kasashe masu zafi.

Shi ma Sakatare na Hukumar Ilimin Fasaha ta Kasa NBTE, Farfesa Idris Muhammad Bugaje, ya ce shirin zai taimaka wajen karfafa horas da kwararrun ma’aikatan lafiya a Najeriya.

Masana da suka halarci bitar sun kuma ba da shawarar a fara aiwatar da shirin a kalla a wata cibiyar kafin karshen shekarar nan.

 

Ibrahim Suleiman/Zaria

Labarai

Labarai5 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai1 day ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi1 day ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara