Connect with us

Kasuwanci

Matan da Mazajensu Suka Rasu Sun Sami Tallafin Kayayyakin Sana’o’i a Jihar Kwara

Published

on

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

Aƙalla matan da mazajensu suka rasu su 600, da matasa ne suka sami tallafin kayan aiki, da na abinci da kyautar kuɗi daga mamba da ke wakiltar Gundumar Ilori ta Kudu a Jihar Kwara, domin su zama masu dogaro da kansu.

A yayin taron ƙarfafawar mai taken “Daga Mafarki zuwa Gaskiya: Shekaru Biyu na Cimma Nasara a Gundumar” (Iwosan Tesiwaju 4.0) mamba da ke wakiltar Gundumar Ilorin Kudu a Majalisar Dokoki ta Jihar Kwara Maryam Yusuf Aladi ta shirya, Shugaban APC na Jihar Kwara, Prince Sunday Fagbemi, ya ce manufar wannan shirin shi ne fitar da mutane daga kangin talauci.

Shugaban jam’iyyar wanda mai ba gwamnan Jihar Kwara shawara kan harkokin siyasa, Sulyman Abubakar, ya wakilta, ya gode wa mambobin jam’iyya bisa goyon bayan da suka nuna ga shugabancin hangen nesa a jihar.

A cewarsa, dukkan mambobin jam’iyya da sauran mazauna jihar za su amfana da mulkin dimokuradiyya kamar yadda jam’iyyar ta yi alkawari.

Prince Fagbemi ya bayyana cewa ƙarfafawa ga matan da mazajensu suka rasu da sauran mutane wani kyakkyawan mataki ne na rage wahalhalun da suke fuskanta.

Ya gode wa Maryam Yusuf Aladi bisa hangen nesanta wajen taimakawa marasa galihu a cikin al’umma.

A jawabinsa, Shugaban Majalisar Dokoki ta Jihar Kwara, Yakubu Danladi-Salihu, wanda Seun Ogunniyi ya wakilta, ya ce a koyaushe Majalisar tana ƙarfafasu wajen ganin suna tallafawa al’umma domin inganta rayuwar talakawa.

Ya yi kira ga sauran mambobi su bi sahun waɗanda suka tallafa wa marasa galihu domin rage rashin aikin yi a cikin al’umma.

A sakonta na alheri, shugabar mata ta APC a Jihar Kwara, Hajiya Falilat Mohammed, ta yabawa ‘yar Majalisar bisa tallawa  waɗanda ke cikin buƙata.

Ta ce da yawa daga cikin waɗanda suka amfana suna buƙatar ƙaramin abu ne kawai don su fara wata sana’a.

Hajiya Falilat ta bukaci waɗanda suka amfana su tabbatar sun yi amfani da kayayyakin da kuɗin da aka ba su yadda ya dace.

A jawabinta, shugabar mata ta APC a majalisar dattawa, Hajiya Tawakalitu Agaka, ta nuna farin ciki da wannan shiri na tallafa wa marayu da marasa galihu.

Ta shawarci waɗanda suka amfana da  kada su sayar da kayan da aka ba su.

A nasa bangaren, Shugaban Karamar Hukumar Ilorin Kudu na Jihar Kwara, Nuhu Podo, ya y> kira ga dukkan mambobin jam’iyya su tabbatar sun samu muhimman takardu kamar lambar shaidar kasa da katin zabe domin su sami karin fa’idodin gwamnati daga matakin jihar da tarayya.

Tunda farko a jawabinta, Maryam Yusuf Aladi, memba mai wakiltar Gundumar Ilorin Kudu a Majalisar Dokoki ta Jihar Kwara, ta ce an yi wannan ƙarfafawa ne don tallafa wa mutanen da ke cikin gundumar.

Ta bukaci waɗanda suka amfana su ɗauki wannan tallafi a matsayin damar fara kasuwanci wanda zai ba su damar tallafa wa iyali.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da: da  Injin Wanki, Injin Busar da kai, Fanka mai amfani da hasken Rana, Injin Niƙa, Keken Dinki da Firiji da sauransu.

 

Labarai

Labarai18 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai19 hours ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai19 hours ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai3 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara