Connect with us

Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kwace Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 82 A Bauchi

Published

on

Daga Alhassan Usman 

Sashen Ayyuka na Tarayya, da ke Yanki na 4 a Bauchi, na Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) wato Zone D, ya kwace kayayyakin fasa-kwauri da darajar harajinsu ta kai sama da Naira Miliyan 82 cikin makonni biyu.

Kwamandan Yankin, Abdullahi Kaila, ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a Bauchi, inda ya ce jami’an sashen yaki da fasa-kwauri sun yi nasarar kwace kayayyakin tsakanin ranakun  8 zuwa 19 ga watan Disamban 2025.

Ya bayyana cewa Sashen na Ayyukan Tarayya ne ke da alhakin aiwatar da dokokin Kwastam, bin manufofin haraji na gwamnati da kuma dakile fasa-kwauri a jihohi tara, wadanda suka hada da Adamawa, Taraba, Bauchi, Gombe, Borno, Yobe, Plateau, Benue da Nasarawa.

Kaila ya kara da cewa an kara karfafa ayyukan yaki da fasa-kwauri a yankin, ta hanyar inganta hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu sa ido, yana mai jaddada cewa irin wannan hadin gwiwar na kara musayar bayanan sirri da aiwatar da ayyukan hadin kai wajen yakar kungiyoyin fasa-kwauri.

Ya bukaci ‘yan kasuwa a yankin da su kasance masu bin doka, su kuma guji haramtaccen kasuwanci, yana mai gargadin cewa ba za a bar wata mafaka ga masu aikata fasa-kwauri ba.

Kwamandan ya kuma ce sashen zai ba da muhimmanci ga wayar da kan jama’a, ta hanyar amfani da kafafen yada labarai da kuma kai ziyara yankuna daban daban, domin fadakar da jama’a game da illar fasa-kwauri ga tattalin arziki da kuma karfafa su su rika kai rahoton haramtattun ayyuka.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara