Connect with us

Kasuwanci

Matan da Mazajensu Suka Rasu Sun Sami Tallafin Kayayyakin Sana’o’i a Jihar Kwara

Published

on

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

Aƙalla matan da mazajensu suka rasu su 600, da matasa ne suka sami tallafin kayan aiki, da na abinci da kyautar kuɗi daga mamba da ke wakiltar Gundumar Ilori ta Kudu a Jihar Kwara, domin su zama masu dogaro da kansu.

A yayin taron ƙarfafawar mai taken “Daga Mafarki zuwa Gaskiya: Shekaru Biyu na Cimma Nasara a Gundumar” (Iwosan Tesiwaju 4.0) mamba da ke wakiltar Gundumar Ilorin Kudu a Majalisar Dokoki ta Jihar Kwara Maryam Yusuf Aladi ta shirya, Shugaban APC na Jihar Kwara, Prince Sunday Fagbemi, ya ce manufar wannan shirin shi ne fitar da mutane daga kangin talauci.

Shugaban jam’iyyar wanda mai ba gwamnan Jihar Kwara shawara kan harkokin siyasa, Sulyman Abubakar, ya wakilta, ya gode wa mambobin jam’iyya bisa goyon bayan da suka nuna ga shugabancin hangen nesa a jihar.

A cewarsa, dukkan mambobin jam’iyya da sauran mazauna jihar za su amfana da mulkin dimokuradiyya kamar yadda jam’iyyar ta yi alkawari.

Prince Fagbemi ya bayyana cewa ƙarfafawa ga matan da mazajensu suka rasu da sauran mutane wani kyakkyawan mataki ne na rage wahalhalun da suke fuskanta.

Ya gode wa Maryam Yusuf Aladi bisa hangen nesanta wajen taimakawa marasa galihu a cikin al’umma.

A jawabinsa, Shugaban Majalisar Dokoki ta Jihar Kwara, Yakubu Danladi-Salihu, wanda Seun Ogunniyi ya wakilta, ya ce a koyaushe Majalisar tana ƙarfafasu wajen ganin suna tallafawa al’umma domin inganta rayuwar talakawa.

Ya yi kira ga sauran mambobi su bi sahun waɗanda suka tallafa wa marasa galihu domin rage rashin aikin yi a cikin al’umma.

A sakonta na alheri, shugabar mata ta APC a Jihar Kwara, Hajiya Falilat Mohammed, ta yabawa ‘yar Majalisar bisa tallawa  waɗanda ke cikin buƙata.

Ta ce da yawa daga cikin waɗanda suka amfana suna buƙatar ƙaramin abu ne kawai don su fara wata sana’a.

Hajiya Falilat ta bukaci waɗanda suka amfana su tabbatar sun yi amfani da kayayyakin da kuɗin da aka ba su yadda ya dace.

A jawabinta, shugabar mata ta APC a majalisar dattawa, Hajiya Tawakalitu Agaka, ta nuna farin ciki da wannan shiri na tallafa wa marayu da marasa galihu.

Ta shawarci waɗanda suka amfana da  kada su sayar da kayan da aka ba su.

A nasa bangaren, Shugaban Karamar Hukumar Ilorin Kudu na Jihar Kwara, Nuhu Podo, ya y> kira ga dukkan mambobin jam’iyya su tabbatar sun samu muhimman takardu kamar lambar shaidar kasa da katin zabe domin su sami karin fa’idodin gwamnati daga matakin jihar da tarayya.

Tunda farko a jawabinta, Maryam Yusuf Aladi, memba mai wakiltar Gundumar Ilorin Kudu a Majalisar Dokoki ta Jihar Kwara, ta ce an yi wannan ƙarfafawa ne don tallafa wa mutanen da ke cikin gundumar.

Ta bukaci waɗanda suka amfana su ɗauki wannan tallafi a matsayin damar fara kasuwanci wanda zai ba su damar tallafa wa iyali.

Kayayyakin da aka raba sun haɗa da: da  Injin Wanki, Injin Busar da kai, Fanka mai amfani da hasken Rana, Injin Niƙa, Keken Dinki da Firiji da sauransu.

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara