Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta Baiwa Kungiyar Tsoffin Sojoji Gagarumar Gudummawa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Kungiyar Tsoffin Sojoji reshen jihar Jigawa ta samu tallafin sama da naira miliyan 40 a wajen taron kaddamar da Gidauniyar Tallafawa Kungiyar na bana, wanda aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayyana matuƙar godiyarsa ga irin sadaukarwar da mambobin Legion suka yi, ciki har da waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen hidimtawa ƙasa.

Ya jaddada cewa irin wannan sadaukarwa za ta ci gaba da kasancewa a tarihin ƙasa, tare da tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa da al’ummar jihar za su ci gaba da nuna godiya da tallafa wa tsoffin sojojin domin samun ingantacciyar rayuwa.

Gwamna Namadi ya sanar da bayar da gudummawar Naira miliyan 10 daga gwamnatin jihar, tare da tasa gudummawar ta Naira miliyan 2. Mataimakin Gwamna, Injiniya Aminu Usman, shi ma ya bayar da Naira miliyan 2, yayin da ƙananan hukumomi 27 na jihar suka bayar da gudummawar haɗin gwiwa ta Naira miliyan 13.

Sauran manyan gudummawa sun haɗa da na mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar, Shugaban Ma’aikatan Gwamnati (Head of Service), Manyan Mataimaka da Masu Ba Gwamna Shawara na Musamman, shugabannin hukumomin tsaro, da kuma Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Correspondents’ Chapel, wadda ta bayar da Naira dubu 100.

A  jawabin, Shugaban Kungiyar Tsoffin Sojojin Nijeriya a Jihar Jigawa, Malam Aliyu Mustapha, ya gode wa gwamnatin jihar da al’ummar jihar baki ɗaya bisa ƙauna, tausayi da girmamawa da suke nuna wa mambobin Legion.

Ya bayyana cewa irin wannan kyakkyawar mu’amala tana ƙara ƙarfafa gwiwar kowa a cikin al’umma, tare da nuna cewa ba a manta da sadaukarwar da suka yi a baya ba.

Ga ’yan uwana tsoffin sojoji, ina tabbatar muku da cewa Gwamnatin Jihar Jigawa na tsaye daram tare da mu,” in ji Shugaban.

Ina matuƙar jin daɗin wannan karamci, kuma ina sake tabbatar da kudurin Kungiyar Tsoffin Sojojin Najeriya na ci gaba da fafutuka da hulɗa tare domin inganta walwalar dukkan mambobin Legion a faɗin jihar.”

 

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara