Connect with us

Labarai

Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Shugaban kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar  tabbatar da ganin cewa kananan hukumonin jihar 27 sun wallafa cikakken kundin kasafin kudadensu cikin zangon farko na sabuwar shekara.

Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, ya bayyana haka ne lokacin tantance kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara na ma’aikatar kananan hukumomi.

Ya kuma yi kira ga ma’aikatar da ta duba batun rashin biyan albashi ga wasu daga cikin nadaddun kansiloli, kasancewar yanzu haka akwai nadaddun kansiloli 21 da ba sa samun albashin su.

Ya kara da cewar, kwamitin ya samu koke kan tsallake albashin wasu ma’aikatan kananan hukumomi sakamakon aikin tantance ma’aikata na IPPS  ta yadda wasu ma’aikatan sun yi ritaya ba tare sun karbi albashin da aka tsallake su ba.

A nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar kananan hikumomin Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya bada tabbacin yin duk abinda ya kamata domin magance wadannan batutuwa.

Ya ce ma’aikatar ta yi kiyasin kashe naira miliyan dubu 13 domin gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a shekarar 2026.

Hannun Giwa, ya kuma bayyana cewar daga cikin manyan ayyuka akwai gyaran ofisoshin shiyya na jami’an duba kananan hukumomi guda 7.

Yana mai cewar za’a kuma kammala aikin ginin sabbin ofisoshi dake kananan hukumomin Babura da Kafin Hausa.

Kazalika, Kwamishinan ya ce za’a sayi motocin aiki da babura ga jami’an duba kananan hukimomi da mataimakansu, tare da kudaden gudanarwa domin ziyarar aiki a lungu da sakon kananan hukumomin jihar 27.

 

Labarai

Labarai19 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai19 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai19 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai19 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai19 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara