Labarai
‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Mata 28 Da Aka Sace A Katsina
Rundunar ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro sun ceto ‘yan matan nan 28 da aka sace daga kauyen Kasai da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Abubakar Sadiq ya sanya wa hannu, ta ce an kubutar da dukkan ‘yan matan ba tare da wani rauni ba.
‘Yan fashin sun yi wa yaran ‘yan shekara takwas zuwa sha biyar kwanton bauna ne a bayan gari, inda suka je dibar itacen da za su kai gida domin yin girki.
Sanarwar ta ce da samun rahoton faruwar lamarin, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aliyu Abubakar, ya tura jami’ai zuwa dajin tare da yin tattaki domin ceto yaran.
Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun yi watsi da yaran ne sakamakon matsin lamba da ‘yan sanda suka yi musu, inda suka gudu suka bar yaran wadanda a halin yanzu suke cikin koshin lafiya.
“Kokarin hadin gwiwa da tawagar ceto ta sa kai, tare da dabarun da rundunar ta dauka, ya sa aka sako dukkan wadanda aka sace”. Inji shi.
“Wannan nasara ta nuna jajircewar rundunar da kuma duk wanda ke da hannu acaiki.n ceton.
Sanarwar ta kara da cewa “Za a ci gaba da kokarin tabbatar da tsaron al’umma da jihar baki daya.
Ismai’l Adamu
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
