Connect with us

Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Bi Sahun Takwarorinsa Na Bada Tallafi Ga Alhazai

Published

on

Gwamnatin jihar Kebbi ta amince da tallafin Naira miliyan daya ga kowane mahajjacin jihar su dubu uku da dari uku da arba’in da hudu domin sauke farali a aikin Hajjin shekarar 2024.

Kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Yakubu Ahmed Birnin Kebbi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai, biyo bayan taron gaggawa na majalisar zartarwar jihar da aka gudanar a ranar Litinin.

Ya ce, hakan ya biyo bayan karin kudin aikin Hajjin 2024 ne da Naira miliyan daya da dubu dari tara da Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta yi.

A cewar sa, za a biya Naira miliyan daya ga kowane maniyyaci da ya kammala biyan kudin aikin Hajjin sa a baya.

Dangane da batun fasa shaguna da sace-sacen hatsi da wasu baragurbi suka yi a babban birnin jihar, Kwamishinan ya ce, gwamnatin jihar ta yi Allahwadai game da hakan.

Alhaji Yakubu BK ya ce gwamnatin jihar ta yi tir da irin wadannan munanan dabi’u domin ba halayyar mutanen jihar ba ne.

Ya kara da cewa, an kafa kwamiti mai mutum 13 a karkashin jagorancin kwamishinan aikin gona don binciki lamarin.

Kwamitin, zai bankado musabbabin wannan  aika-aikar, tare da tantance mutanen da ke da hannu tare da ba da shawarar hanyoyin hana sake aukuwar hakan.

Shima da yake magana akan lamarin, kwamishinan noma da albarkatun kasa, Alhaji Shehu Muazu, ya shaidawa manema labarai cewa, kayan agajin da aka wawashe na gidauniyar Dangote ce ba na gwamnatin jihar ba.

Abdullahi Tukur

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai8 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai9 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai22 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi4 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara