Connect with us

Labarai

‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Mata 28 Da Aka Sace A Katsina

Published

on

Rundunar ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro sun ceto ‘yan matan nan  28 da aka sace daga kauyen Kasai da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Abubakar Sadiq ya sanya wa hannu, ta ce an kubutar da dukkan ‘yan matan ba tare da wani rauni ba.

‘Yan fashin sun yi wa yaran ‘yan shekara takwas zuwa sha biyar kwanton bauna ne a bayan gari, inda suka je dibar itacen da za su kai gida domin yin girki.

Sanarwar ta ce da samun rahoton faruwar lamarin, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aliyu Abubakar, ya tura jami’ai zuwa dajin tare da yin tattaki domin ceto yaran.

Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun yi watsi da yaran ne sakamakon matsin lamba da ‘yan sanda suka yi musu, inda suka gudu suka bar  yaran wadanda a halin yanzu suke cikin koshin lafiya.

Kokarin hadin gwiwa da tawagar ceto ta sa kai, tare da dabarun da rundunar ta dauka, ya sa aka sako dukkan wadanda aka sace”. Inji shi.

“Wannan nasara ta nuna jajircewar rundunar da kuma duk wanda ke da hannu acaiki.n ceton.

Sanarwar ta kara da cewa “Za a ci gaba da kokarin tabbatar da  tsaron al’umma da jihar baki daya.

 

Ismai’l Adamu

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai8 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai8 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai21 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara