Connect with us

Fasaha

Shirin Uwargidan Shugaban Kasa Ya Fara Aiki A Arewacin Nijeriya

Published

on

Mutane masu lalurar nakasa su 100 za su amfana da shirin gwamnatin jihar Plateau na naira dubu 100 kowanensu domin bunkasa samarda abinci.

Uwargudan shugaban kasa Sanata Olureni Tinubu ta bayyana wannan gudummuwa a wane banagre na Shirin sabonta fata da ofishinta ke gudanarwa.

Wannan. Shirin dai na sabunta fata, ofishin uwargidan shugaban kasa ne ya fito da shi domin tallafawa mata da masu lalurar nakasa da kula da ilimin mata da lafiya da aikin gona da karfafa mudu gwiwa su Iya dogaro da kansu.

Uwargidan shugaban kasar Sanata Oluremi Tinubu Kuma shugabar wannan shirin ta fada wajen kaddamar shi a yankin arewa ta tsakiya cewa, an gabatar da Shirin a kowane yanki in Banda yankin kudu maso kudu da za a gabatar Nan gaba.

Uwargidan shugaban kasar wacce ta sami wakilcin uwargidan shugaban ma’aikatan fadar Shuganan kasa kuma daraktar Shirin karfafa al’umma Mrs. Salamatu Gbajabiamila, Sanata Tinubu ta za a raba naira miliyan 10 ga mata 20 daga yankin Arewa ta tsakiya domin su ma su Sami damar gudanar akin gona don su ciyarda kansu.

Don haka Tayi kira ga wadanda zasu amfana da shirin su kashe kudaden su ta hanyar da ta dace.

A jawabinta tunda farko, uwargidan gwamnan Jihar Plateau Mrs. Helen Mutfwang wacce ta sami wakilcin kwamishiniyar ma’aikatar ilimi mai zurfi Mrs. Kachallom Gang ta bayyana mata a matsayjn kashin bayan kowace al’umma don haka tayi kira ga sauran matan gwamnonin jahohi suma su aiwatar da irin wannan Shirin a jahohinsu.

A sakonnin su daban daban, uwargidan gwamnan jihar kwara kuma shugabar Shirin ta jahohin ta tsakiya Farfesa Olufolake Abdurrazak wacce ta Sami wakilcin uwargidan shugaban majalisar wakilai Hajiya Sa’adatu da Kuma gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang dukkanin su bakinsu ya zo daya wajen godiya ga uwargidan shugaban kasa Sanata Olufemi Tinubu saboda wannan tallafin nata ga masu lalurar nakasa da ke tsakanin al’umma

Daga cikin abubuwan DA aka gabatar wajen wannan Taron shi ne gabatar da cakin kudi naira miliyan 10 ga jahohin arewa ta tsakiya da birnin Abuja da zasu amfana da shirin.

A yankin Arewa Maso Gabas Kuwa, Sanata Tinubu ta mika cek na Naira miliyan goma ga wadanda su ne matan shugabannin shiri a jihohinsu domin ci gaba da rabawa mata manoma a shirin.

Uwargidan mataimakin shugaban kasa Hajiya Nana Kashim Shettima ta wakilci uwargidan shugaban kasar, ta roki wadanda suka amfana da su kara fadada ayyukan su na noma a fannin kiwon dabbobi, kiwon kifi ko kiwon kaji domin bayar da tasu gudummawar wajen samar da abinci na gida da kasa baki daya.

Ta bayyana kwarin gwiwar cewa shirin ba wai kawai zai canza rayuwar daidaikun wadanda suka ci gajiyar shirin ba ne, har ma zai taimaka wajen samar da wadataccen abinci a yankin Arewa maso Gabas.

A Arewa Maso Yamma Kuwa da aka gabatar a Birnin Kbbi, Uwargidan Shugaban kasa ta bayyana cewa shirin zai tallafa wa mata dari da arba’in a harkar noma da kudi naira dubu dari biyar kowacce kuma za a tallafa wa mutum dari daya masu bukata ta musamman da Naira dubu dari kowane.

Uwargidan kakakin majalisar wakilai Fatima Tajuddeen Abbas ta wakilce ta, ta ce shirin zai hada kai da ma’aikatar noma ta tarayya domin tabbatar da samar da abinci da kuma dorewar abinci a kasar.

Don haka ta bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudin da kayan aikin da aka ba su ta hanyar tallafa wa a samarda abinci a kasar.

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasiru Idris, a nata jawabin, ta bada nata tallafa, inda ta tallafa wa kowane mutum dari da arba’in da suka amfana da injinan fanfo mai amfani da hasken rana sannan kowane mai bukata ta musamman da kayan abinci iri-iri.

Josiah Buzum/Dauda Iliya/Abdullahi Tukur/ Shafii Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 days ago

Muna Tare Da Gwamnatin Bola Tinubu – Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa

Gamayyar Kungiyoyin MatasanJihohin Arewa Na 19 Sun Ce ko kadan ba sa goyon bayan Zanga-zangar, domin Barazana ce Ga Tsaron...

Labarai2 days ago

‘Yansanda Sun Sake Kama Masu Zanga-Zanga 70 A Uganda

An kama masu zanga-zanga da dama wadanda suka halarci wani haramtaccen gangami da aka gudanar a Kampala babban birnin Uganda,...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Wa Masu Shirin Zanga-Zanga Gargadi

Rundunar Tsaron Najeriya ta gargadi masu shirin zanga-zangar yaki da tsadar rayuwa a Najeriya ta ce sojoji ba za su...

Labarai2 days ago

Olympics: ‘Yan Matan Najeriya Za Su Kara Da Na Brazil

A yau Alhamis ne ƙungiyar Super Falcons ta ‘yan ƙwallon matan Najeriya za su kara da takwarorinsu na Brazil a...

Labarai2 days ago

Sanatocin Arewa Sun Jinjinawa Tinubu Bisa Amincewa Da Kafa Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa rattaba hannu kan kudirin hukumar raya yankin Arewa maso...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Bukatar Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomi

Majalisar zartaswar jihar Jigawa ta amince da bukatar hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar, na gudanar da zaben kananan...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu  kan kudirin doka don hanzarta samar da ci gaba a shiyyoyin kasar nan....

Labarai3 days ago

Za’a Fara Wasannin Olympics A Faransa

Yayin da ake dab da fara gasar wasannin motsa jiki ta bazara wato Olympic, ta shekarar 2024 a birnin Paris...

Labarai3 days ago

‘Yan Jaridan Kenya Za Su Yi Zanga-Zangar Adawa Da Cin Zalin ‘Yansanda

Ƴanjarida a ƙasar Kenya za su gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar domin nuna adawa da zargin cin zalin da...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Rabon Tallafi Ga Kananan ‘Yan Kasuwa A Jigawa

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bukaci matasa da su guji yin zanga-zanga a kasa. Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya...

Mafi Shahara