Connect with us

Fasaha

Shirin Uwargidan Shugaban Kasa Ya Fara Aiki A Arewacin Nijeriya

Published

on

Mutane masu lalurar nakasa su 100 za su amfana da shirin gwamnatin jihar Plateau na naira dubu 100 kowanensu domin bunkasa samarda abinci.

Uwargudan shugaban kasa Sanata Olureni Tinubu ta bayyana wannan gudummuwa a wane banagre na Shirin sabonta fata da ofishinta ke gudanarwa.

Wannan. Shirin dai na sabunta fata, ofishin uwargidan shugaban kasa ne ya fito da shi domin tallafawa mata da masu lalurar nakasa da kula da ilimin mata da lafiya da aikin gona da karfafa mudu gwiwa su Iya dogaro da kansu.

Uwargidan shugaban kasar Sanata Oluremi Tinubu Kuma shugabar wannan shirin ta fada wajen kaddamar shi a yankin arewa ta tsakiya cewa, an gabatar da Shirin a kowane yanki in Banda yankin kudu maso kudu da za a gabatar Nan gaba.

Uwargidan shugaban kasar wacce ta sami wakilcin uwargidan shugaban ma’aikatan fadar Shuganan kasa kuma daraktar Shirin karfafa al’umma Mrs. Salamatu Gbajabiamila, Sanata Tinubu ta za a raba naira miliyan 10 ga mata 20 daga yankin Arewa ta tsakiya domin su ma su Sami damar gudanar akin gona don su ciyarda kansu.

Don haka Tayi kira ga wadanda zasu amfana da shirin su kashe kudaden su ta hanyar da ta dace.

A jawabinta tunda farko, uwargidan gwamnan Jihar Plateau Mrs. Helen Mutfwang wacce ta sami wakilcin kwamishiniyar ma’aikatar ilimi mai zurfi Mrs. Kachallom Gang ta bayyana mata a matsayjn kashin bayan kowace al’umma don haka tayi kira ga sauran matan gwamnonin jahohi suma su aiwatar da irin wannan Shirin a jahohinsu.

A sakonnin su daban daban, uwargidan gwamnan jihar kwara kuma shugabar Shirin ta jahohin ta tsakiya Farfesa Olufolake Abdurrazak wacce ta Sami wakilcin uwargidan shugaban majalisar wakilai Hajiya Sa’adatu da Kuma gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang dukkanin su bakinsu ya zo daya wajen godiya ga uwargidan shugaban kasa Sanata Olufemi Tinubu saboda wannan tallafin nata ga masu lalurar nakasa da ke tsakanin al’umma

Daga cikin abubuwan DA aka gabatar wajen wannan Taron shi ne gabatar da cakin kudi naira miliyan 10 ga jahohin arewa ta tsakiya da birnin Abuja da zasu amfana da shirin.

A yankin Arewa Maso Gabas Kuwa, Sanata Tinubu ta mika cek na Naira miliyan goma ga wadanda su ne matan shugabannin shiri a jihohinsu domin ci gaba da rabawa mata manoma a shirin.

Uwargidan mataimakin shugaban kasa Hajiya Nana Kashim Shettima ta wakilci uwargidan shugaban kasar, ta roki wadanda suka amfana da su kara fadada ayyukan su na noma a fannin kiwon dabbobi, kiwon kifi ko kiwon kaji domin bayar da tasu gudummawar wajen samar da abinci na gida da kasa baki daya.

Ta bayyana kwarin gwiwar cewa shirin ba wai kawai zai canza rayuwar daidaikun wadanda suka ci gajiyar shirin ba ne, har ma zai taimaka wajen samar da wadataccen abinci a yankin Arewa maso Gabas.

A Arewa Maso Yamma Kuwa da aka gabatar a Birnin Kbbi, Uwargidan Shugaban kasa ta bayyana cewa shirin zai tallafa wa mata dari da arba’in a harkar noma da kudi naira dubu dari biyar kowacce kuma za a tallafa wa mutum dari daya masu bukata ta musamman da Naira dubu dari kowane.

Uwargidan kakakin majalisar wakilai Fatima Tajuddeen Abbas ta wakilce ta, ta ce shirin zai hada kai da ma’aikatar noma ta tarayya domin tabbatar da samar da abinci da kuma dorewar abinci a kasar.

Don haka ta bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudin da kayan aikin da aka ba su ta hanyar tallafa wa a samarda abinci a kasar.

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasiru Idris, a nata jawabin, ta bada nata tallafa, inda ta tallafa wa kowane mutum dari da arba’in da suka amfana da injinan fanfo mai amfani da hasken rana sannan kowane mai bukata ta musamman da kayan abinci iri-iri.

Josiah Buzum/Dauda Iliya/Abdullahi Tukur/ Shafii Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai11 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi1 week ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci1 week ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Mafi Shahara